KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

“anas! Jaguwa ya kira sunansa  gbdy  yarinyar nan bata da manners  “gaban anas ya fadi sakamakon ganin tanweer a  tsaye a bayan jaguwa rungume da hannuwanta anas ya Kai hannunsa zai nuna masa bayansa jaguwa ya buge masa hannun “Kaine ka kawo maganar dan haka ka bari na gama kafin ka shigo da wata “sam sam yarinyar  bata da tarbiya iyayenta basu koyar  daita yadda ake girmama babba ba  da kace mata cas zatace maka kul , ko da yake taya zatayi tarbiya haihuwa tayis reinon tayis  tashin turai kasan baza’a  sameta da cikakkiyar  tarbiya amman Misali ace  da gaske   zan yi  soyayya da  wata mace  da itace  farko  kodan disvarging  dinta da nayi amman bazanyi ba yana gama fad’ar haka ya juya da niyyar  barin gurin  turus yayi zuciyarsa na karkarwa sakamakon idanunsu da suka tsarke cikin juna.”

Mmn sudais????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????

PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.

????️20

…..juyowa  yayi  ya  Kalli  anas dake   tsaye  a bayansa yana tmbyrsa   da  kwayar  Idanunshi  dake  cike  da matsanacin firgici  ko  taji  abinda  ya fad’a , shima da  kwayar  Idanunshi  ya bashi amsa  alamun  taji  komai daya fad’a  a yanzu  .” ya subhanallah ya   furta  a  kasan  makoshinsa  yana  mai  sake juyowa  Inda take  tsaye ,   tana  nan  tsaye kmr wacce  aka  dasata  agurin sai dai zuwa  wannan lokacin babu komai acikin kwayar idanunta sai  tsananin  firgici  dake  tattare  da  tashin  hankali .
  Muryarta  na  rawa  tace  “me naji  ka  furtawa  abokinka yanzu ? “mafarki  nake
ko  kuwa  karya ne ? “
taku  d’aya  ta K’ara  tana sake  cewa “kace  karya  kunnuwana suka  jiyo  min ba  gaskiya ba ?” shiru  yayi  yana  kallonta zuciyarsa na  wani  irin  rawa  dan  gbdy  ya gama  rikicewa   bai  so  taji  abinda ya shiga tsakaninsu  ba “ka fad’a min gaskiya  Adnan da gaske kayi disvarging  dina  ? ta  fad’a tana wani  irin sheshekar kuka kmr ranta  zai  bar gangar jikinta “idan  gaske ne kayi disvarging dina  a yaushe kenan kayi da  ni ban  san da zaman hakan   ba ?” still  shiru  yayi  qirjinsa na cigaba da  bugawa  da karfin gaske  , sai dai wannan karon yayi  k’okarin  Kai hannunsa jikinta  domin  kamota , tayi saurin  buge  masa hannu “dan Allah  ka  fad’a min cewar karya ne  ba gaskiya bane dan zuciyata bazata  iya d’aukar wannan sabon  tashin hankalin ba ?”.
ta  k’arasa  maganar  tana cakumar  wuyar  rigarsa da hannuwanta duka  ta matse  masa  wuya  gam da iyakacin karfinta  tana  fidda  zazzafan numfashi .”

anas  na  ganin  haka ya lalla’ba sun sun ya gudu ya barsu su karata , dan  bai san ta yadda zai shawo  kan  matsalar ba , shi  da yayi  silar amsar budurcinta sai  yasan duk  yadda zai yi  ya  shawo  kanta   .” Ka  fad’a  min cewar karya ne  Adnan bakayi komai dani  ba?  dan  Allah  karka ce min  kayi  disvarging dina….”  wannan  kalmar  kawai
take fad’a  tana  sake  maimaitawa  .  rungumeta  yayi   tsam  ajikinsa  yana  sakin  numfashi  babu  shiri  ta sakar masa wuya saboda ba  karamin runguma yayi mata ba , ya  Kai  bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma rad’a mata mgn cikin  sanyayyiyar muryarshi   me  kashe  gabobin jiki   “da  gaske ne tanweer amman  kece  silar   Komai  daya faru ,kece  da kanki kika kawo min  kanki  batare da nayi niyyar aikata  hakan ba”.

“Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun  ta  furta cikin tsanani tashin hankali, zamewa tayi ajikinsa ta kwalla wata razananniyar qara mai  sauti  da tasa gbdy gidan ya amsa  tana  ihu  ta zube kasa warwas  tana  kuka da birgima da  sauri  ya durkusa gabanta ya rikota  gam jikinsa na rawa tamkar  mazari   yace “wallahi ba da  son  raina  nayi ba kece kika bukaci  hakan “.
“ni ….!
Ta  furta a  tsawace tana watsa masa wani mugun kallo ,ya gyada mata Kai alamun “eh !
“na shiga uku na lalace ni surayya  Adnan ka cuceni taya zaka  min haka? “taya ma zan kawo maka kaina wallahi ban san na aikata hakan ba karya kake min wallahi bazan ta’ba aikata hakan ba saboda Ina qaunar  budurcina fiyye da komai dake cikin duniyar nan”  .
kuka  tanweer take sosai kamar ranta  zai fita ya bar gangar jikinta ta mike tsaye ta soma tafiya  cikin tsananin tashin hankali  tsabar gigicewa hanyar special  room dinsa ta nufa har tayi taku uku ya biyota da hanzari  ya fixgota da karfi ya sake  mannata  a faffadan qirjinsa “am  really sorry for…..” ai bata bari ya karasa ba ta shiga dukan  qirjinsa da iyakacin karfinta  tana tsine masa tana mai  sake fashewa da wani kuka . kamkameta yayi sosai ajikinsa duk  ya  rud’e  ya gigice sai zufa yake  fitarwa “ka sakar min jiki bana  son  kusancinmu tare ,  tsanarsa  take son yi  irin tsanar da bata  ta’ba  wani halitta ba amman  tsanar  taki sauka acikin  zuciyarta .”

Muryarta cike da kuka tace “a tunanina na tsira daga kaidinka a she ban tsira ba ,” me yasa kamin haka  Adnan ? wallahi  nasan bana haiyacina bancin haka babu abinda zai sa na baka kaina , Kuma ko duk  duniya zasu  taru akaina  bazan taba yarda da nice na kawo maka kaina ba  sai  dai  idan wani abu ka bani na sha har kayi nasarar akaina “.
shiru yayi kawai yana sauraronta yana tunanin yadda zai ku’butar da kanshi agurinta take ya tuna da cctv  na bangarensa  dan  haka yay  gauggawar zareta ajikinsa ya riko tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita nan fa ta turje tana cewa “babu Inda zani ka rabu dani wata hadaddiyar tsawa ya buga mata yana cewa  “muje !
iya abinda bakinsa ya iya fad’a kenan ya cigaba da tafiya bai tsaya akoina ba sai a d’akinsa ya zaunar daita tana wani irin kuka me ta’ba zuciya .”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button