KUSKUREN BAYA 1 TO 48

ta mike ta shiga bayi ta d’auki lokaci sannan ta fito rike da towel tana goge gashin kanta har lokacin yana nan sai dai zuwa lokacin ya shirya mata Komai nata , ta wucesa ta zauna gaban dress mirror ta d’auki cum tana k’okarin taje gashin kanta.
ta cikin mirror taga ya mike kafin ta sauke numfashi har ya k’araso bayanta ya tsaya ya amshi cum din hannunta yana kallonta ta cikin mirrow sosai ta xuba masa Idanunta .
ya d’auke kwayar idanunshi akanta ya cigaba da taje mata gashinta baki sitik me sheki ga tsawo kmr na yaran larabawa yana mugun qaunar gashi a rayuwarsa , ya d’auki man gashinsa ya shafa mata yana jin tsinkewar zuciya ba zai raba d’ayan biyu ba na rabuwa daita ne bayan ya gama shafa mata mai ya cigaba da taje mata gashin ita Kuwa Jin take kamar yana sake kunno mata wutar soayyyarsa ce ,ajiyar zuciyar data sauke da karfi yasashi sake kallonta ta cikin mirrow murmushi ya sakar mata har dimple dinsa na lotsawa ganin yadda gbdy yanayinta ya canza wani iri take ji ajikinta .”
a hankali ta rike hannusa da yake taje mata gashi dashi ta waiwayo gbdy ta fuskancesa Shima ita yake kallo yana jin wani sanyin na ratsa sansar jikinsa yatsina fuska tayi tana cigaba da kallonsa”ya’akayi ko Ina miki da zafi ne? Kamar bazata fada masa abinda take ji a gabobin jikinta ba Amman yadda ya kafeta da idanu yasa ta mike tsaye tana motsa labbanta “wani iri naje ji a sansar jiki….”
bata k’arasa maganar ba tajita a faffadan qirjinsa ya rungumeta tsam ajikinsa yana fidda numfashi atare qirjinsu ya dinga bugawa da karfin gaske tayi yunkurin barin jikinsa taji ya sake matseta gam idanunshi a lumshe kamar yadda nata yake a hankali ya dinga jin kasala me had’e da sha’awa yana kashe masa duk wata gaba ta jikinsa yana jin kamar ya canza lokaci komawarta ko yaki maidata gbdy su dangwama a haka “lokaci na tafiya fa …”
“nasani kin matsu ki tafi kou ?
ya fada yana zareta ajikinsa tare da had’e girar sama data kasa “Allah ba wai na matsu bane Ina son naga dad dina ai zamu dinga had’uwa “Bai zama lallai ba tunda bazaki iya auran dan fashi ba ” ya fad’a tare da juya wa ya bar d’akin.
shiru tayi cikin damuwa ita dai duk runtse bazata auresa da wannan sana’ar da yake ba amman muddin ya canza aiki sai Inda karfinta ya kare itama zatayi confused din iyayenta akan aurenta da ib su amince ta auresa .
“zaka daina wannan sana’ar tabbas zaka daina Kuma kana sona tunda har kayi tunanin zaka iya aurena inshallahu zamuyi aure sai mun Tarawa amminka jikoki masu yawa kwanciya tayi akan gado tana fidda numfashi sama sama . abubuwan da ya dinga mata daren jiya suka shiga dawo mata daki daki .
Sai laasar sannan jaguwa ya shigo ya kamota ya rungumeta na kusan minti goma sannan ya zaunar daita akan stood ya tattara gashin kanta ya tamke mata da ribbon ya d’auki mayafin rigar jikinta ya yafa mata ya d’auki jakar kayanta ya nufi kofar fita “muje ko jiki a sanyaye ta soma d’aga ka’fafunta kmr wacce ake tsomawa acikin ruwa sanyi ,duk sai taji kuzarinta yayi kasa komai ya fita aranta a falo ya tsaya ya ajiye jakarta ya bud’e fridge ya d’auki fresh milk da chocolate cake ya mika mata ta girgiza masa Kai alamun bata ci bai sake cewa Komai ba ya zauna ya fara ci ,haushi kmr ya kasheta taso ya sake yi mata mgn dan yadda ya had’e fuskarsa abun har tsoro ya bata ,bai gama ci ba ya ajiye sauran ya mike tana ganin ya mike ta juya kawai taji ya fixgota ya had’eta da jikinshi yana sauke numfashi tanweer ta dan lumshe idanunta tana Jin yadda numfashinta dana jaguwa ke gauraya kusan minti goma suna rungume da juna sannan ya sausauta rikon da yayi mata ya had’e fuskarsu guri d’aya suna shakar numfashin juna .
harshensa ya dan fito dashi yana lasar lip’s dinta a karshe ya had’e bakinsu ya fara tsotsa sai daya tsotsa sosai sannan ya sakar mata baki still bai ce mata ummm ba bare Uhmmm ya sake d’aukar jakarta yayi gaba tana biye dashi a baya har suka fito haraban gidan yaransa na ganinsa duk suka mike zasu nufo Inda yake da hannu ya tsai dasu ya bude mata gaban motarsa range Rover ash colour ta shiga ta zauna tana kallon haraban gidan datayi rayuwa wata uku a ciki ,bazata manta da komai daya faru daita acikin gidan ba,komai ya zamo tarihi a rayuwarta .”
bata Ankara ba taji tashin motar me gadi ya bud’e masa suka fita daga gidan tun da suka hau titi babu Wanda yayi magana tafiyar minti goma sukayi ta Kai hannunta ta d’auki wayarsa ta mika masa “ka bude min bai ce mata Komai ba ya amsa ya bude mata ya mika mata ya cigaba da tukinsa ta shiga message sako ta turawa tsohon layinta dake cikin karamar wayarta sannan ta ajiye wayar a inda ta dauka .
tafiya me dan nisa sukayi dan sai byn magrib suka k’araso royar stream yayi parking nesa da gidan man tsakanin inda yake zai Kai tafiyar minti goma tun daga nesa ya hango minister tsaye yana baza idanu yaga ta Inda tanweer zata bayyana shiru yayi yana karewa gurin kallon tsab”ki fita ga mahaifinki can ya fad’a yana nuna mata Inda yake tsaye ,shiru tayi kmr bazata fito ba “ki fita mana kina bata min lokaci, ta kallesa kmr zatayi kuka dan har hawaye sun cika mata Ido ta yunkura da kyar zata tashi ya fixgota jikinsa ya rungumeta tsam kuka ta fashe masa dashi.
a hankali ya shiga shafa kanta zuwa bayanta “is okay ki kukan please ya Isa haka ke da zakiyi farinciki zaki kwana a gida tare da iyayenki da dinbin masoya shine zaki dinga hasarar hawayenki dan zaki rabu dan fashi ” girgiza masa Kai ta shiga yi tana sheshekar kuka ya d’ago habarta Yana kallon kwayar idanunta da fuskarta dake kwance shabe shabe da ruwan hawaye.
tsadadden murmushinsa ya sakar mata “why tanweer ?ya zaki min hk?idan kina son na dinga tunaki a duk bayan second biyu ki daina kukan nan .
da sauri ta shiga goge hawayenta ya Kai bakinsa yayi mata light kiss “oya kije ga dad dinki can ya matsu bai d’aura idanunshi akanki ba ya saketa ta bud’e kofa zata fita yace “karki manta da alkwarinki ” ta dawo kadan tana dubansa kwayar idanunta d’auke da tmby “na zaki sa akamani mana dan naga kin saci numbeta” dukan wasa ta Kai wa qirjinsa “Kai ko Allah shiryeka “Ameen na gode da addua “,Ki kula da kanki sosai ki daina tsiwa da rashin kunya dan akwai irinmu dayawa acikin garin nan “Kaima ka kular min da kanka akan wannan sa’anartaka banason ka fad’a hannun police ” Faduwa da nasara duk daya ne agurina duk wasu kwalaye dake dakona bazasu iya komai ba har sai idan na tare dani ne suka bada hasken cutar dani.”
“karfin zuciyarka na burgeni ta Kalli yatsun hannunta ta ciro zoben silver me shegen kyau wanda kakarta wacce ta haifi mahaiyar ce ta bata zoben, ta kamo yatsun hannunsa ta zira a karamin dan yatsansa dan anan kawai zai zauna “Ina sonka adnan !”
ta fad’a tana lumshe masa idanunta bai ce mata Komai ba bare tayi tunanin zai bata amsa.
Jin yayi shiru yana kallon zoben da tasa masa tace ” muje ka rakani bansan gurin nan ba “, numfashi ya sauke yace ” muje anything for you ta sake yunkurawa ta fito Shima ya bud’e bangaren da yake ya fito .
tafiya kad’ai suka yi ya juya yana cewa “iya nan zan tsaya ” tayi saurin juyowa da sauri ta kamosa tare da nuna masa gefen kumatunta da hannunta alamar yayi kissing dinta ” kiss yayi mata ya juya ta sake biyosa ta nuna masa d’ayan gefe “oh my goodness tanweer lokaci na tafiya fa kar dad dinki ya wuce ya d’auka karya nake masa “.
“sorry! sorry!! daga wannan shikenan ya furzar da iska sannan yayi mata har zai sake juyawa ta sake riko sa “wai meye haka ne ? Yayi mgnr a fusace “,ai Kaine Kaki yin aikinka da kyau saura me mahimmancin tayi mgnr cike da shagwaba tana nuna masa bakinta daidai lips dinta .
Numfashi ya sauke da karfi ya janyota gbdy ya rungumeta tsam ajikinsa ya hade bakinsu guri d’aya ya fara tsotsan bakinta nan idanun mutane sukayi musu chaaa tun da suka fara dramar soyayyarsu mutane suke biye dasu jiki a sanyaye ya zare bakinsa “,bye tanweer ya fad’a yana juyawa ta tsaya shiru tana kallon bayansa bai juyo ba duk da jikinsa ya bashi bata wuce ba .
jikinta a sanyaye ta juya ta soma taku a hankali adaidai lokacin da jaguwa ya juyo a natse ya tsurawa bayanta Ido yana kallon yadda take taku a hankali tana rausaya har ta Iso gurin mahaifinta ,tana gama k’arasawa gurin mahaifinta ta zube ajikinsa .
Jaguwa ya lumshe idanunshi ya sake juyawa ya karasa Inda motarsa take pake ya shiga ya tayar sai dai hakan nan yaji ya kasa control din motar ya daura duka hannuwansa akan stearing ….”
????????????????????????
KUSKUREN BAYA
????????????????
????????????????????????