KUSKUREN BAYA

KUSKUREN BAYA 1 TO 48

Mmn sudais????????????????????????
KUSKUREN BAYA
     ????????????????
????????????????????????

PAID BOOK

 WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
          

WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin na kudi ne  mai bukata karanta shi  ya tura 500 ta wannan  account number din  1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert  domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za’ayi  sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu  a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.

????️25

zama   jaguwa  ya  cigaba   da  yi  rike  da  waya   zuciyarsa  na zafi da  farfasa  a qalla  ya kusan minti  goma  yana  tunanin maganganunta,”  bai  san me yasa  zai  damu  kansa  akan cikin  ba , cikin  ma  da bashi da  tabbacin  tana d’auke dashi .
wani   dogon   tsaki  yaja  yana   sake  kiran  layinta , babu ‘bata  lokaci   ta   d’auka  qirjinta na bugawa  fat  fat “Ke ni zakiwa wulakacin ? “
shiru  tayi  taki  ce masa komai  sai  dai  zuciyarta  ke wani irin  bugawa da sauri sauri .
“har  kin  isa   ki dinga  farfad’a min  magana son  ranki  ?”
ya sake tmbyrta tare da jan  tsaki “har  ma  da  kashe min waya ? “shiru  tayi  still  cikin  tsananin  tashin  hankali tana tunanin  abinda  zata sake fad’a masa  wanda  zai sake d’aga masa  hankali  sai dai bata kai ga tattara  abinda zata  fada  masa ba  ta  tsikayi  muryarsa na dukan   dodon  kunnenta.
“dan  kinga ina lalla’baki  shine zaki d’auka ko ina  jin  tsoron ki haifi cikin ne ? “to  kar  allah yasa ki cire cikin ai cikin ba ajikina  yake  ba  idan akwai shi kenan  dan  haka  ko ki cire ko Karki  cire ruwanki sannan  matsalarki ce  bata Adnan  .
ba Adnan za’a dinga kwatance dashi ba , sannan ba shi zai rasa mai aurensa ba . aurenki  ne dai bazan  yi ba  kije ki nemi abokin rayuwarki  dan ni  tuni na amince da  zabin mahaifiyata aikin  banza Kawai  ki jira  ki gani  idan  zan sake  nemanki”.
ya k’arasa maganar yana jan dogon  tsaki sannan ya katse Kiran  yana fidda wani wahalallen numfashi ,yasa hannunsa  d’aya ya dafe goshinsa yana  jin  zafi  da ciwo a ransa, shiru yay na  second goma  qirjinsa  da  gangar jikinsa na  rawa   gbdy  sai   yaji  kimai ya tsaya  masa  guri  daya  ya shiga tunanin abinda yayi mata  a ganin zuciyarsa   bai  kyauta mata  ba daya farfad’a mata son  ranshi  dan  bata  cancaci  ya fad’a  mata  magangun daya fad’a mata ba ,ita din wata aba ce mai daraja da  kima a  rayuwarsa. amman daya  tuna irin maganganun  data  fad’a masa da irin mugun fatan da tai masa a mintunan da suka gabata  sai  ya  dawo  haiyacinsa ,  komai ya dawo  masa daidai, qirjinsa da gangar jikinsa da suka d’auki rawa  suka  daidaita  yaga  mai ma yayi mata ai bai mata komai ba  . “

Bangaren  tanwer  kuwa maganganunsa sun  daki Kunnuwanta  sosai sannan sun wuce  har  cikin zuciyarta, gbdy ya  kunno  mata  wutar  damuwar da take dannewa  acikin  zuciyarta  ,Kawai sai ji  hawaye yazo idanunta  ya fara zuba  akan  kuncinta, a hankali ta fara  rare kuka mara sauti qirjinta na zafi  “Allah ka gani ba wai  nayi  masa haka dan  na wulakatanshi bane , “na yi dan na raunata zuciyarsa,na yine  ko zai saduda ya zubar da makamansa ya  canza rayuwarsa  darajan  tace  bata zubar ba suyi aure  ,ashe  wata sabuwar maseefa  ta jefa kanta ciki tayi maganar a fili tana sheshekan kuka  “wayyo Allah  ka d’auki raina  na  huta  da wannan rayuwar  da nake ” wani  zafi take a kahon zuciyarta sam ba taji kashi  daya na son da take masa ya  rugu  sai ma qaruwa da son shi yayi acikin zuciyarta , tana  sonshi    muddin zai aureta zatai  confuse din  iyayenta  akwai  hanyoyi  da dama da idan ta bullo dasu dolensu  su  hakura su rungumi  nata qaddarar su aura mata shi amman shi kuji abinda yake fad’a  mata har ma ya amince da zabin mahaifiyarsa ita ko  oho  zama  tayi ta  cigaba da rera  kukanta tare da rafka uban tagumi cikin zullumi da rashin  sanin  madafa .”

tana  cikin  wannan halin  rukayya ta shigo d’akin ganin idanun  tanwer   na  zubar da ruwan   hawaye yasa ta karasa shigowa  d’akin da sauri  tana cewa “lafiya  tanwer menene Kuma ?”
Rukayya ta samu guri gefenta ta zauna ta riko hannuwanta duka  cikin  nata  tana dubanta cike da tausayawa , runtse idanunta tanweer  tayi sai ga wasu hawayen  sharrrrrr.”
“wallahi ina cikin damuwa  rukayya ,ina cikin tashin hankali  na rasa  yadda  zanyi da wannan rayuwar da nake  ciki , komai ya canza  min rukayya  ina ma rayuwata ta baya  zama dawo  , “ina ma ban dawo kasar nan ba”..
Rukayya  ta numfasa tace” haka ne  kina cikin  damuwa da jarabawar  rayuwa  tanwer  amman  kiyi  hakuri da sannu komai zai  daidaita ,”sannan   kiyi kokari ki  rage damuwar nan duk  da  tasan komai dake faruwa  daita amman taki fitowa ta bayyana mata .
” ki kara  imani  da qaddara komai ya faru da bawa a rubuce yake  bawa bai isa ya gujewa qaddararsa, rayuwar bawa tana tattare da qaddarori ne  kawai dai  Allah  ya bamu Ikon cinye jarabawarmu  rukayya   ta  fadi  haka ne dan takaita maganar .
“nima ina son na rage tunanin  Adnan acikin zuciyata  amman na rasa dalili da tunaninsa  kullum sai gaba  yake , wallahi ina  masa wani irin so da bansan ranar da zan daina shi  ba , kuma bazan taba fidda raina akanshi  ba sai  ranar dana ji an shafa fatihan  aurensa ta k’arasa maganar tana  mai  runtse idanunta.”

“Aure ma zaiyi shine kika zauna kina tunaninsa “? tanweer ta gyada mata kai alamun “eh! “gskiya dai ni aganina ki manta dashi kawai ki cigaba da rayuwarki tunda ma aure zai yi ki manta shi kiyi  addua sai Allah yayi miki sauyi na alkhairi  .
Tanweer ta gyara zama  tana kallonta “na  fahimceki yar’uwarta zan cigaba da addua na gode da shawarki “to amman banason kina damuwa, tanweer ta sake yin murmushin wanda ciwonsa yafi kuka gbdy kana kallonta kaga damuwa attare daita duk ta fita haiyacinta soyayya ya canza mata rayuwarta muryarta a raunane tace  “na gode rukayya inshallahu zan daina .
.” Ki  kwantar  da hankalinki  kinji dan Allah karki  sake daga hankalinki  akansa Ki  fara  nemi zabin Allah kiyi k’okari kiyi  istahara domin neman  zabin  Allah “rukayya ko ya min  wani irin adduar  istaharar da zanyi”.?
“zan koya miki , mu nemi zabin Allah  bamu  sani ba ko akwai alkhairi atsakaninku  idan babu idan  kinyi zaki ga komai ya tafi daidai   amman Karki  yarda  ki bari  wani yayi miki  kiyi  da kanki ,zaki iya yi kullum  idan  zaki kwanta raka biyu zaki yi  sai kiyi sallama sai kiyi addaurki ta istahara inshallahu zaki ga cigaba a rayuwarki  hatta wannan radadin da kike ji akanshi  zaki rage jinsa .”
Jiki a sanyaye   tanwer ta janyo handbag dinta ta Ciro biro da farar takarda ta mikawa rukayya.
ta  amsa ta fara rubuta mata adduar “Allahumma inni astakhiruka bi ilmika,wa astaqdiruka bi kudiratika wa as’aluka min fadilikal azim,Fa innaka taqdiru Wala aqdiru,wata alamun wala ahlamu ,Wa anta allamul guyub, Allahumma in kunta tahlamu ana hazal amuru anan sai ki fadi bukatarki sannan ki cigaba,Khairulli Fi dini wama ashi wa akibati amri,Ajilihi wa ajilihi,Faqdurhuli wa yasshirhuli summa barikli Fi,Wa in kunta ta’alamu inna hazal amri sharruli Fi dini wama ashi wa akibati amri ajilihi wa ajilihi,Fasrifhu anni wasrifni anhu,Waqdurliyal khaira haisu kana summa ardini bihi.”inshallahu inshallahu tanweer sai kinga komai ya daidai ki mikawa Allah alamirinki zai isar miki wallahi idan Adnan rabonki ne zai dawo da kafafunsa har ma kuyi aure “na gode rukayya inshallahu zanyi  ,sun dade suna hira rukayya na deba mata kewa , bata ta’ba sanin zama da mutun guri d’aya yana kawowa rayuwar mutun sauyi ba sai data dawo gida ta iske rukayya , rukayya na k’okarin  kawar mata da  dukkanin damuwarta tare da bata shawarwari masu kyau  .”
Da misalin karfe goma na dare kowa  ya  shige  d’akinsa  tanweer  ta shiga bathroom dinta tayi  alwala ta fito ta sanya dogon hijab dinta tare da  shimfida sallaya tayi sallahrta raka biyu sannan ta gabatar da adduar istaharar da rukayya ta rubuta mata sannan ta nemi guri ta kwanta  akan  katifa  zuciyarta cike da tunanin Adnan  kala kala a hankali wani bacci mai ni’imal ya d’auketa .” 

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192Next page

Leave a Reply

Back to top button