FITAR RANA COMPLETE HAUSA NOVEL

FITAR RANA COMPLETE HAUSA NOVEL

FITAR RANA COMPLETE HAUSA NOVEL

Gameda najaha kuwa bawai munafurcinta bai bashi mamaki bane,but he really dont care koda ace hakan bai faru ba dama aransa yana da niyyar dakatar da ita daga zuwa Gidan datakeyi tana damunshi,inba dan kwanciyar hanklin wasime ba da hala baxata taba samun sakin fuskarshi ba, rawan kanta da yarantarta sosai ya qundireshi.
Daurewa kawai yakey yana kulata amma har cikin ransa baso yakei ba.

Kuma Dalilin dayasa kenan jiya yay ma wasime fada dan ta nitsu ta koyi abinci,sai dazu dayakejinsu suna fada ya fahimci ashe ma duk karya najaha take shirga masa akan wasime..

Furzan iska ya saki ta bakinshi yana mai shafe kansa izuwa fiskan shi cikin nazarin matakin dazai dauka akan najaha

A bangaren Wasime kuwa da mugun gudu ta fita,not minding the heavy storm dake sama dan wani irin bakin haddari ne a sama yay baki kirin ga iska mai karfi yana kadawa sosai ,gudu take tana kuka bata tsaya a koina ba Har saida ta isa gaban gidan su najaha.

A fannin najahar kuwa ko dataje gidansu kuka ta dinga tana complain din abunda wasime ta mata dan abun bakaramin ci mata rai yay ba musammn ma abunda tay mata na kara sugar nan, mamanta ta ne ta dinga lallabarta tace tay hakuri wasar ma yanzu aka farashi,tace daga zarar angama ruwa ta shirya taje gidan ta bawa wasime hakuri,tace hakan ne zaisa taheer ya kara yadda da ita daga nan kuma zata gaya mata yadda zata rama abunda wasime tay mata,tace “akanki sai munsa ya tsaneta ya dena yarda da ita kwata kwata…kiyi shiru abunki autana ai dani takeja. Ba ita ta fara kawo wasar ba?to insha Allahu mu zamu kai mata wasan nata har karshe..kisa ranki a inuwa snn kisani
Aurenki da taheer kamar anyi angama,karamr yarinya kamar wasime bata isa tahana afkuwar komi ba. Najaha dole ki zage damtse ki nuna mata ke ba irinta bace.
Kinaji ko?

Najaha ta goge fuskarta tace “naji mama…can sai tayo wani jimmm kamarban cakuleta ta firgita ta Dada rushewa da kuka tanayi kamar ana dukanta,.. cikin kukar tace”mama dan Allah kitaimaka min wallhy ni shi kawai nakeso,yaa taheer ya hadu .wai baza’a iya daura mana auren mu tun yanzu bane..aiba dolene bane saina kara girma ko mama?..nide wallh ina mutuwar sonshi kuma shi kawai zan aura dan Allah mama kitemaka min rarrashinta maman ta dingayi tana bata baki.

Wasime tana tsayawa a kofar gidansun aka fara zabga ruwan sama kamar da bakin kwarya
Lokacin maman najahan ta fito kenan zata kulle kofar gidansu saitaganta

Da balain mamaki a fuskarta tace”Wasima ?wann ba wasima bace meya faru meya kawoki nan cikin ruwan nan,sauri tay ta karaso tana kkrin janyeta daga cikin ruwan

A hatsale wasime ta Fauce hannunta cikin fushi tace”ni kije kice ma najaha tafito kawai…ni wajenta na zo..ba wajenki ba..inta isa sunanta najaha tazo ta fuskance ni.

Turus Mamar najaha ta tsaya da wani irin azabar mamakin zuciya irinta wasime..taga babu alaman tsoro ko razana atattre da ita.

Ruwa nakan dukanta’ tana bari kar kar kar amma bashi yahanata tsayawa tay kyam cikin masifa ba,ranta ya mugun baci,kirjinta bakaramin tafasa yakeyi
Ba.

Maman najaha dakejin bazata iya tsayawa da ita acikin ruwan sama ba tace “To kishigo ciki mana kya tsaya a acikin ruwa snn kice lallai sai najaha ta fito ta ganki ahaka?

Tace eh dolenta ne ta fito,kuma Ni Bazan shigo cikin gidanku ba,Allah ya kiyayemin…kice mata kawai tafito..

Maman najaha bata kara cewa komi ba ta koma cikin gidanta tahau dokawa najaha kira

Najaha tana fitowa tace
Toh ga marar kunyar kawanki can awaje tazo nan wai lallai saidai ace miki kifito

Da Baya baya najaha ta ja tay can gefe Tana girgiza kanta a tsorace tace”Uhm uhm mama ni wallh bazanje wasime ta kashe ni ba…shegiyar karfi ne gareta..cewa ma tay zata min lilis ni gaskiya kije kawai kice mata bana gida.

Maman dake cikke da jin takaicin ruwan ciki irin na yarta take tahauta da fada tana cewa ke wallhy kin cika tsoro shiyasa ma zata rainaki,ai dolenki kuwa kije kiji mezatace miki,aida abunda zatace miki yanzu zamu san ta indaa zamu kama bakin zarenmu,kedai dakikiyace najaha..sam baki da wayo,kekan tir kamar ba acikina kika fito ba?..inma tsoron dukn kikeji to shikenan muje tare ni zan rakaki ai intasan wata bata san wata ba.

..Najaha batace uffan dukansu suka fito a tare.

Najaha dake ta dau hudubar mamanta,da gwarin gwiwarta tayo kan wasime cikin sauri tana cewa “Wasime me ya kawoki gidanmu kukan me kike?nide
Dan Allah ki shigo ciki muyi magana mu fahimce juna,ruwa fa akeyi ni wlh bazan iya tsayawa anan acikin ruwa ba Kizo kawai
…tana fadin hakan ta wani jawo hannun wasime da niyyar kaita gida

Wani hatsallen Ihu wasime tasaka mata tana mai tureta a hargitse cikin wani haukataccen salon bori

Ja da baya najaha tay tana kallonta

…ni karki sake tabani
Munafuka kawai..kinje kinsa yayana yana cemin nayi mishi karya da munafurci bayan duk kece kika fara,dabaki munafurce ni ba nima ai bazan miki ba.
Allah ya isamin najaha
saita cigaba da kukanta
Ahankli tana kukan tace wallh bazan taba yafe miki azzaluma.

Cikin sanyin jiki da karyewar zuciya najaha tace” kai Wasime..
kuskure fa nayi dan Allah kidena fushi dani kiyafe min ,wallh Son da nakeyi ma yayanki ne ya jawo haka,Wasime ina matukar kaunar yaya taheer,ko mama na shitake sob in aura.

Nida ke fa kawayene meye na daukar abun dana miki da zafi,harda ramawa.Wasime yakamata ace kin fahimci uzurina,kinsan fa ance babu abunda so baya sakawa,Wasime Kin dau abun nan da zafi..ki dubi girman Allah….
Wani tayau taji an
tsinka mata wata gawaurtaccen mari akan fuskanta

Ahaukace wasime ta birkice mata tana cewa An dauka da zafin,an dauka din,kuma Banace karki kara kiran suna na ba?..Ke ni ba kawarki bane…Dan kinga kawai nazo nan shine zaki soma gayamin maganan banza wai kina son yayana? ni badan inji zancen banzanki naxo nan ba mahaukaciya kawai..

yayana ne yace ince miki nice na kara miki sugar a tea dinki,shine yace ince miki kiyi hkri baran kara ba..

Ni wallhi dakiyi hakri da karkiyi duk uwarsu daya ubansu daya, nide karki kara zuwa kofar gidanmu ni ba kawarki bace,karki kuma kara zuwa inda nake ko a makranta munafuka kawai…

Juyawa tayi zata tafi maman najahar ta karaso tana kwalla mata kira “ke wasime meye haka?kin haukace ne…

Kota kulata ta tayi wucewarta dan wani lungu ta je ta buya inda basa kallonta. Akan gwiwarta ta tsuguna ta dinga kuka mai tsuma tana tuna maganganun najaha datace wai yayanta take so,haka kawai taji wannan maganan ya birkita ta,wani irin ruwan kishi mai tsanani takeji mai kuma tukukin zafi tana jan zuciyarta sama sama tana kukan kamar ranta zai fita.

Nemanta suka dingayi har suka gaji suka dena

Cahn sannan ta fito ta zauna agefen dakalin gidansun ta takure kanta waje guda tadinga sheka kuka acikin ruwa.

Tun ficewarta taheer ya fito nemanta dan baiyi tsammnin da taurin kan tan nan data nuna masa dazu har zata rusuna taje gidan su najahan ba

Nemanta ya dingayi a wasu wajajen can anjima
kawai ya dawo ta gidan su najahar koda zai ganta,yana isowa daf ya dallara hasken motarsa nan da nan yaganta akofar gidan su najahar ta takure kanta waje guda acikin ruwan sama tana tikar kuka

Da hargitsatsen sauri yay parking ya taho cikin sauri ya fixgota tsaye

Ihu ta fasa masa mai kara tanacewa nika kyaleni nika kyaleni aina bata hakurin ba abinda kace bakenan?…nika kyaleni..ai ba sona kakeyi ba,najaha kawai kake so..ka kyaleni kawai nima bana sonka…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191Next page

Leave a Reply

Back to top button