GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Ido ta maida kan Hajia Mama dake gurnani kamar macijiya.

Jim kaɗan ta fito.
Cike da son gano wani abu Ummi ke binta da ido, amman ta kasa gano komai domin Shatu ta iye takunta, ta fito kamar ba itaba gaba tayi.

Kana suka nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.
Suna shiga ta miƙowa Shatu da Hibba hannu kusa da ita ta ajiyesu.
Bayan sun gaisane ta kallesu tare da cewa.
“Azumi ya boyeku da yake ku ragwagene”.
Murmushi sukayi tare da cewa.
“Kai Gimbiya jiya nefa kawai bamu zoba”.
Cikin kula Lamiɗo dake shigowa yanzu zai sabunta al’wala zai wuce masallaci yace.
“Shatu matar malam bauɗeɗɗe”.
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai.
Hibba ce tace.
“Sai na gaya mishi”.
Dariya sukayi kana suka sallamesu suka tafi ganin lokacin sallan yayi.
Har sunje bakin ƙofa Gimbiya Aminatu tace.
“Yauwa Jakadiya kayan miyanku da saura ko ya ƙare?”.
Cikin rusunawa tace.
“A’a da saura sosaima”.
Kai ta gyaɗa kana suka tafi.
A hanyarsu ba komawane Shatu tace.
“Ummi wanne kayan miyan ne?”.
Cikin sanyi tace.
“To ba kince bakya son na Hajia Mama ba, shine ita kuma Gimbiya Aminatu ta haɗo miki komai yanzu dasu muke amfani ai”.
Cikin gamsuwa tace.
“To wancan ɗinfa ya akayi dashi?”.
“Umaymah ta tafi dashi duka”.
Hibba ta faɗa mata.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Ba matsala”.

Nan suka tafi suna salla suka shiga kitchen yau harda Hibba.

Sannu-sannu dai bata hana zuwa sai dai a daɗe ba’a jeba.

Yau an cika azumi goma. Gobe za’a shiga goma na wuya, an gama na marmari.

Yau kuma makara Shatu tayi.
Ganin har su Jalal sun zone yasa Ummi ta nufi ɗakinsu.
Ai kuwa kan gado ta hangosu.
Tadasu tayi kana ta fito.
Tana cewa.
“Shatu kiyi sauri kizo ki kaiwa Sheykh nashi”.
Kusan a tare suka diro ƙasa.
Brush kawai sukayi suka fito.
Da ƙaton hijabin ta fito.
Tana zuwa Dinning area Ummi ta miƙa mata tray’n abincin nasa.

Amsa tayi ya juya ta nufi falonshi.

Tsaye ta sameshi gaban show glass ɗin dake gefen Fridge ɗinsa dake Dinning area,
Cup ne a hannunshi cike da madarar gongoni da molt a haɗe.
A hankali ta wuceshi kaɗan ta ajiye tray’n.
Kana ta juyo da nufin sauƙowa, taku ɗaya tayi a na biyu ta iso gabanshi kenan.
Aka saki bindigar shaidar huɗu da rabi tayi.
Wani irin zabura tayi tare da af….!

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, domin shiga Normal group wanda a wata ɗaya za’a, gama Part one. Ko kima kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank, domin samun shiga Special Group wanda a sati biyu cakal za’a gama Part two da izinin ubangiji, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853297.

Ke mai haushi kin turo ɗarinki uku, kinzo kinata haushi, nace ki turo ac no ɗinki in maida miki kuɗinki kin tsaya yimin tumasanci shiyasa nayi Black ɗinki, a rashin Sa’a na haɗa da number ki na goge. Kuma baki Turo ac na na meda miki shi ba. To Alhamdulillah a take a lokacin nayi miki sadaka da ɗarinki uku, ubangijina shine shaidata, banci kuɗinki ba, nasan zakiga PAGE ɗin sabida akwai waɗanda basu san darajar Allah da Manzonsa da iyayensuba, zasu fitar, to kiji ni Shatu na sauƙe nauyin ɗarinki uku.

                    By
        *GARKUWAR FULANI*Cikin tsananin firgita, da tsinkewar zuciya da tsoro, tare da kerman jiki, ta juyo ta fuskanci inda yake tsaye tare da abkawa jikinshi.

Cikin abinda bai gaza one second ba tamkar gilmawar walƙiya ya janye jikinshi ya kauce gefe.
Hakan yasa ta faɗa jikin show glass ta ruggumeshi gam-gam cikin tsuma da karkarwa tare da sa hannunta duka biyu ta riƙe kanta, tana mai cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani’imanwakil, Auzubikalimatillahi ta’ammati minsherri makalaƙa.”

Tanayi cikin ɗan ɗaga murya mai baiyana firgicin da take ciki.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin masifeffen dariya ne ya taso masa tun daga ƙasan zuciyarshi har zuwa kan lips ɗinshi dole ya taune lip ɗin shi na ƙasa.
Kana sai ya gimtse ya murtuƙe fuska cikin tsare gida yace.
“Karki fasamin abuna!”.
Sai lokacin hankalinta ya dawo jikinta.
Janye jikinta tayi daga jikin show glass ɗin da abkawar da tayi kanshi marfinshi ya ɗan tsage.
Nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe da ƙarfi.
Kana ta tura baki sannan ta juya ta fara tafiya tana ƙunƙunin.
“Allah ya isana banzan al’ada a rinƙa razana mutun anasa hanjin cikina na hautsunewa”.
Baki ya taɓe kana ya zauna bisa kujerar ya jawo tray’n ya ɗibi abincin tuƙeƙen tuwo ne da miyar kase.

Tana fitowa sukayi sahur ɗin a gaggauce sabida lokacin ya ɗan ƙara to.

Washe garin da rana bayan anyi sallan azahar.
Ya shigo kamar ko yaushe.
A falo ya samu Ummi da Hibba ita kuwa Shatu tana ɗakinta tana karatu so take ta samu izu uku a wunin yau ɗin.
Gefen su ya ratsa kana ya zauna bisa kujerar zamanshi.
Bayan sun mishi sannu da zuwa ne, ya kalli Hibba cikin kula yace.
“Muhibbat ya azumin”.
Cikin langwaɓe kai tace.
“Da wuya”.
Kanshi ya jinjina kana yace.
“Jeki kira Aunty Juwairiyya”.
To tace tare da miƙewa da sauri ta fita.
Shi kuwa wayarshi ya ciro ya kira Jalal dasu Imaran yace suzo su sameshi a falo.

Jim kaɗan duk suka shigo.
Key ya zaro daga al’jihun tattausan jallabiyar dake ƙasan al’kyabbar jikinshi ya miƙa wa Jamil tare da cewa.
“Ɗauko min briefcase a kan Bedside drower’n.”
To yace kana ya juya ya tafi.
Shi kuwa Ummi ya kalla tare da cewa.
“Ummi me dame kuke buƙata ne?”.
Cikin kulawa tace.
“Akwai komai, sai zam-zam ɗin kane ya ƙare saura baifi gora biyarba”.

Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
“Ba matsala zai isa”.
Lokacin Jamil ya iso. Miƙa mishi jakar yayi, tare da zaunawa gefenshi.
Shi kuwa buɗe jakar yayi.
Murmushi Jamil yayi ganin tana ciƙe maƙil da rafan dubu-dubu sabbi dal-dal.
Rafa huɗu ya miƙawa Jamil hakama Jalal da Imran da Sulaiman.
Sannan ya kallesu tare da cewa.
“Kuje KMC plaza ku zabi kayan sallan.
Sai ya kuma kalli Aunty Juwairiyya yace.
“Aunty Juwairiyya, kuje tare dasu, da Ya Jafar ayi yadda aka saba.
Sannan ku zaɓi abin buƙatar ku.”
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
“To mu gode, kuma za’ayi yadda kace.”
Sai kuma ya kalli Ummi yace.
“Ummi kada ki manta da su Saratu”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“In Sha Allah babu abinda za’a mance”.
Kai ya jinjina kana ya zaro rafan guda biyar ya miƙa mata, sannan ya miƙa wa Aunty Juwairiyya wasu rafofin kana ya bawa Hibba biyu.
Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu.

Washe gari kuwa da safe, suka shirya tsab zasu fita.
Aunty Juwairiyya ta Ummi cikin yin ƙasa da murya tace.
“Ko zan kirawo Shatu mu tafi tare da ita ne?”.
Da sauri Ummi tace.
“A a mijinta baice muje da itaba mujata mu tafi. Muje dai mu zaɓo mata duk abinda takeso”.
Cikin gamsuwa da hakan tace to.

Hibba kuwa cikin sanyi tace.
“Ayyah Ummi muje da ita”.
Fitowar Shatu ne ta samesu a tsaye cikin shirin tafi yasa ta kalli Ummi cikin sauri tace.
“Ummi ina zakuje?”.
“KMC plaza”.
Ta Bata amsa a taƙaice cikin sanyi tace.
“Nima inzo muje, in samu in fita insha iskan woje”.
Jalal ne ya ɗan kalleta tare da cewa.
“Boss ya hana”. Ido ta zuba mishi kana ta juya ta kalli Ummi cikin sanyi tace.
“Shike nan Ummi kuje, Allah kiyaye hanya.”
Amin Amin sukace har sun juya zasu tafi sai kuma tace.
“Ayyah Ummi dan Allah karku daɗe”.
To sukace kana suka fita.

Shiru ta zauna a falon ba kowa hakane yasa ta kunna TV tashar Zee world.
Wani film mai daɗi ta samu sukeyi, sai dai bata san forkonshiba, bisa alamu duk sabone.
Konciya tayi bisa 3 str tana kallo wayarta na hannunta.
Tana mgna da Rafi’a.

A haka bacci yayi awon gaba da ita.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button