GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Suna tafiya cikin ƴar faffaɗan hanyar da bishiyoyin namijin gwanda yayi musu ƙawanya,
shiyasa wurin yayi sanyi.

A hankali ya kalleta lokacin da suka iso.
Bakin ƙofar Gimbiya Aminatu.
tare da cewa.
“Umaymah me zanyi a ciki?”.
Hannunta tasa ta kamo nashi.
Kawai ta kutsa kai ciki. Dole ya bita a baya.
Yana saka ƙafarsa cikin falon yaji zuciyarshi ta buga,
da ƙarfi, lokaci ɗaya ta fara harbawa da sauri-sauri.
Cikin sanyi yace.
“Umaymah barni a nan”.
Bata kulashi ba taci gaba da janshi tayi har bakin ƙofar falon Lamiɗo.
wani irin rumtse idanunshi yayi yin yadda zuciyarshi ke barazar fashewa.
Da sallama a bakinta, suka shiga.
Yayinda Lamiɗo da Abbanshi suka amsa mata.
Cikin wani irin azabebben bugun da zuciyarshi keyi, yasa ƙafarshi cikin falon.
yayinda Umaymah ke riƙe da hannunshi tana mishi jagora har zuwa gaban Lamiɗo da Galadima da Abbanshi da kuma Malaminshi Malam Abubakar.
Kana ta tsaya dashi kusa da Aysha tare da rusunawa.
Yayinda shi kuma cikin fargabar yadda ƙirjinshi keyi ya rusa a hankali ya zauna bisa tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a wurin.
Dib, dab, dib, dab, dib, dab. Haka zuciyarshi keyi.
yayinda itama Aysha da bai lura da ita Bama haka zuciyarta keyi,
sabida jin an mutun ya zauna kusa da ita.

A hankali ya lumshe idonshi, sabida bugawar da zuciyoyinsu keyi a tare yasa, ƙarfin nashi bugun ya ɗan ragu kaɗan.

Cikin nitsuwa ya kalli Abbanshi kanshi a sunkuye yace.
“Barka da safiya Abba”.
Cikin kula yace.
“Barka dai”.
Sai ya kuma kalli Malamin nashi cikin kamala yace.
“Allah hokke sabbugo, Malam Barka da zuwa ya gida?”.
Cikin nitsuwa Dattijan yayi murmushi tare da cewa.
“Alhamdulillah Sheykh Jabeer ya hidima”.
Alhamdulillah yace, kana ya kalli Lamiɗo da Galadima.
sai kuma ya kauda kanshi.
murmushi Galadima yayi tare da cewa.
“Mu bazaka gaishemu ba kenan?”.
Ɗan tsuke fuskarsa yayi tare da cewa.
“Gaggawa dai aikin shaiɗan ne”.
Murmushi Lamiɗo yayi sabida ya fahimci duk abinda zasuyi,
sai ya cisu gyara ta kuma fuskar gsky.
Galadima ne yace.
“To ni bari in gaisheka Ina kwana”.
Kanshi ya jinina mishi tare da cewa.
“Kayiwa kanka tanadin lada ashirin, a madadin kaɗan da zaka samu in ni na ɗaga maka gaisuwar.
Lfyta lau Alhamdulillah.”
Ya ƙarishe mgnar da amsa gaisuwar.
Dariya sukayi kana, ya kalli Lamiɗo a daƙile yace.
“Ina sauri dan inada aikin yi, menene kasa aka jawoni nan”.
Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda Abbanshi da Malaminshi bazasu jiba.
Kana ya ɗan muskuta ya matsa gefe yayi nesa da Aysha sabida wani tsalle da yakeji zuciyarshi nayi, a madadin bugun da takeyi kafin ya zauna kusa da ita.
Cikin zuba musu ido.
Lamiɗo yayi murmushi sabida sunyi masifar dacewa da juna, shigarsu da ta zamo iri ɗaya tayi matuƙar yi musu kyau.
Cikin wasa irin na kaka da jika yace.
“Ga amaryar taka baku gaisaba, ku gaisa sai ka kaita kuje ka gabatar da ita”.
Fuskarshi a haɗe yace.
“Hakan addinine ko al’ada?”.
Da sauri Galadima yace.
“Al’adace kuma sai kayi ta”.
Ta gefen ido ya kalli Galadima tare da cewa.
“Da ba Galadima za’a bakaba, da sarkin raya al’adu za’a baka”.
Shiru yayi jin Abbanshi na cewa.
“Allah ya bamu nisan kwana, kaima watan watarana a gabanka yaranka zasuyi min haka Muhammad”.
Cikin yin ƙasa da kai cikin girmamawa da karrama mgnar mahaifin nashi yace.
“Sun isa! Suyi maka haka in barsu”.
Murmushi Malam Abubakar yayi tare da cewa.
“Kamar yadda ka isaba”.
Shiru yayi gane manufarsu.
Jin duk sunyi shiru ne, yasashi ɗago kai ya kallesu.
Suma shi suka zubawa ido, da sauri yayi ƙasa da kanshi.
Ita kuwa Aysha shiru tayi tamkar ruwa ya cinyeta, tanajin yadda suke musayan kalamai. Sai dai bata fahimtarsu domin, tuno nata ahlin.

Gyaran muryan da Abbansa yayine yasashi ɗago kai ya kalleshi.

Cikin bada umarni Abba ya nuna mishi Aysha tare da cewa.
“Kama hannunta kuje, ka gabatar da ita, ka fara daga sashin ƙannen Lamiɗo, sai na Mamanku, daga nan kuje wurin Gimbiya Saudatu,
dama sauran matansu Babanku Nasiru”.
Bisa dole yace.
“To kana ya yunƙa ya miƙa,
da sauri Umaymah ta miƙe tazo ta miƙar da Aysha.
kana ta kamo hannunta ta miƙa mishi alamun ya riƙe hannunta.
Cikin tsuke fuskarsa da kwaɓeta tamkar zai ɗaura hannunshi a ka ya kurma ihu.
Ya zuba mata ido. Muryar Abbanshi ce ta katse tsayuwar da yayi kamar an dashi.
“Riƙe hannunta ku je”. A hankali ya ware tafin hannunshi da Umaymah ta kamo
kana lokacin guda yaji zuciyarshi tana tsalle da harbawa, kamar dai tana mararin wani abu.
Hannun Aysha Umaymah tasa mishi cikin nashi tare da meda yatsunshi ta rumtsesu.
Dam-daradam-dam haka zuciyarshi tayi wani masifeffen bugun mai kama da na aradu kana tafara wani irin tsalle.
Ita kuwa Aysha, wani irin tsuma jikinta ya fara lokacin da taji tattausan yatsun hannunshi da fatar tafin hannunshi ya rumtse nata.
Hannun wani irin masifeffen tsoro da kunyane suka diro mata, a lokaci guda.
Shi kuwa Sheykh wani irin asirtace kuma ɓoyeyyen dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai sanyi, jin gaba ɗaya zuciyarshi ta koma ta nitsu tabar wannan tsinkewar da bugawar da tsalle tayi lib a cikin ƙirjinsa.
Jin muryar Jakadiya ne yasa, Sheykh Jabeer, yin ƙarfin halin ɗaga ƙafarshi ta dama.
Jin ya ɗan yi gabane yasa itama, ta ɗaga ƙafarta ta hagu, sai hakan ya bada wata dama ta musamman, ya zama suna ɗaga ƙafafuwan su, a tare kana suna taku a jere.
Sai dai shi ɗin ya ɗan kereta kaɗan.

“Masha Allah. Tabarakallah,”. Sune kalaman da Umaymah ke Maimaitawa, lokacin da take biye dasu a baya.

Lamiɗo da kanshi da Galadima sunga wani irin dacewa na musamman a tsakin Muhammad Jabeer da Aysha.
Abba kuwa murmushi yakeyi mai baiyana jin daɗi.
Malam kuwa, Addu’o’in yaketa jero musu na fatan al’khairi da zaman lafiya da nitsuwa da samun zuriya ɗayyiba.

A hankali suke taku yayinda kowa zuciyarshi ke bin takun sawunsa,
A haka suka fito babban falon Gimbiya Aminatu nan suka samu Ummi. Tana ganinsu ta miƙe da tsauri tayi gabansu, hadimai hudu cikin na Gimbiya Aminatu kuwa, sukayi bayan Umaymah dake bayansu.

Shi kuwa Sheykh Jabeer suna fitowa yayi wani irin saurin sake hannunta tare da janye nashi,
Sabida shi ji yake tsikar jikinsa na tashi tamkar ya riƙe wutan lantarki ne sabida masifar tsuma da yaki naman jikinsa nayi.
Murmushi Umaymah tayi ganin still dai suna tafiya a jere a jere suna wani irin taku mai ƙayatarwa.

Suna fitowa, suka samu sallama a bakin mashigar wurin.
Nan ya shaida musu, duk sashukan gidajen anje anyi sallama dasu an kuma basu daman shiga.

Tafiya kaɗan sukayi daga sashin Gimbiya Aminatu, ta gefen hagunshi,
suka ɓullo farfajiyar wani babban part,
Jakadiyarsu na gaba suna biye da ita a baya, Umaymah na biye dasu.
A hankali suke taku cikin ƙasaita hadimai da fadawa na mara musu baya.
Suna shiga ciki, suka samuwa wata dattijuwar tsohuwa mai tarin shekaru.
Cikin murmushin da muryar tsufa tace.
“Malamai magada annabawa, lallai yau inada babban baƙo da babbar baƙuwa.”
A hankali suke tafiya har zuwa gabanta, inda take zaune bisa tattausan carpet hadimanta na kewaye da ita.
wanda biyu daga cikinsu, suka tashi da sauri suka kawo ababen motsa baki suka jera a gabansu.

Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya kalli tsohuwar da take matar ga Galadima.
Cikin kula yace.
“Barka da safiya Innano”. Cike da kula tace.
“Barka dai Malam Muhammad, mun samu ƙaruwa ko”.
Kanshi ya gyaɗa mata a hankali haka yasa duk basu ganiba sai ita da yake gabanta.
“Cikin muryar tsufa tace.
“Allah ya sanya al’khairi. Ya baku zaman lafiya. Yasa matarkace iya rai da mutuwa. Ya azurtaku da zuriya ɗayyiba.”
Da Sauri Umaymah ta amsa da Amin Amin hakama sauran baki ɗayansu.
Ita kuwa Shatu, cikin saisaita nitsuwarta ta ɗan kalli tsohuwar tare da cewa.
“Ina kwana”.
Murmushi tayi tare da kai hannunta ta kamo hannun Shatu, tafin hannunta ta buɗe ta zuba musu ido, na yan wasu ɗakiƙu kana tace.
“Lafiya lau, ya baƙu ta?”.
A hankali tace.
“Alhamdulillah”. Jakadiyarsu ce ta ɗan rusuna tare da cewa.
“Mun barki lfy”.
Kai ta gyaɗa kana tayiwa hadimanta umarni su miƙo kyautar da take gadon masarautarsun ce farin gyale ne mai kyau da taushi.
Umaymah ce ta amsa ta miƙa hadiman dake bayanta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button