GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Jalal, Jamil, Haroon, Jafar, kuwa duk suna can Dinning area kan dinning table sunayin breakfast.

A jere suka fito falon shida Barrister Kamal.

Suna isowa tsakiyar falon.
Cikin wani irin taku mai cike da ƙasaita da rashin tsoro.
Ya kalli Gimbiya Saudatu dake zaune bisa kujerar zamanshi.
Yatsunshi biyu ya haɗa ya kaɗa mata tare da mata alamun tashi min kan kujera.
Cikin wani irin kallo mai nuna tsantsar fushi da tsana da zazzafan ƙiyayya ta fara mgna cikin ɗaga sauti tace.
“Hegen yaro mai idanun mujiya, Ni kakeyiwa wannan iskancin dan kan uwar..!”.
Kasa ƙarisa zagin da tayi nufin yi tayi jin yana cewa.
“Kan uwarki ko? Ki ƙara sa mana kikaga ikon wanda ya hana mata gemu ya baiwa maza!
Maza tashi min kan kujerar zama tunda ba wancan jiɓeɓɓen tsohon akun bane seyota”.

Wani irin zabura Baba Nasiru yayi tare da ɗaga hannu zai kifeshi da mari, kamar a mafarki yaji an riƙe mishi hannunshi da sauri ya juyo.
Ido ya zaro cike da mamakin ganin wanda ya riƙe mishi hannunshi cikin tafasar zuciya da ƙuna yace.
“J…..”

                           By
            *GARKUWAR FULANI*

Cikin wani zare ido na masifa yace.
“Jalal ni ka riƙe wa hannu”.
Shima idon ya zare tare da cewa.
“Ba iya rikeshi kaɗai zanyi ba, in dai zai taɓa lfyar ɗan uwana a gaban idona, datseshi zanyi gaba ɗaya in wurgar”. Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da yarfa hannunshi.
Wani irin asirtaccen murmushi Barrister Kamal, yayi tare da kallon ɗan shi Sulaiman hannunshi ya dunƙule ya jinjina wa Sulaiman ɗin.
Kana suka koma suka zauna bisa kujera.
Shi kuwa Jabeer hannun ya nunawa Gimbiya Saudatu alamun ta tashi.
Mirtsitsi tayi tare da gyara zamanta.
Wani irin firgitacen tsawan da Jalal ya danna matane yasa, ta miƙe tsaye ba tare datasan ta miƙa ɗin ba.

Cikin ƙasaita Jabeer ya baza tattausar al’kyabbar jikinshi,
Kana ya matso ya zauna bisa kujerar ƙafarshi ɗaya ya ɗora bisa ɗaya.
Gyara hiramin kanshi yayi tare dayin gyaran murya kana ya kalli ƙannen mahaifin nashi kauda kanshi yayi ganin yadda suke wani irin cika da batse sun cika sunyi tamtsan da fushi.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu zama tayi a kujerar dake kallon tashi
kujerar.
Itama ɗaura ƙafa ɗaya tayi kan ɗaya.
Cikin iya tijara ta watso sabbin jaridu gabanshi.
Jaridar bankaɗa da kuma kamfanin jaridar hantsi wato leƙa gidan kuwa.
Murmushin muguntan tayi tare da cewa.
“Ga sakamakon sa insa da kayi dani jiya, na yau kuma shima yana nan tafe.
Nayi maka murna darajar labarin ya kai matsayin da shine a shafin forko na jaridun”.
Da sauri Jalal ya sunkuyo yasa hannunshi ya ɗauki jaridar banƙaɗa.
Jiki na tsuma ya ɗago ya kalli Gimbiya Saudatu cikin tashin hankali yace.
“Wannan ƙarya ne, da babu jahilin da zai yarda dashi, wlh bazaku taɓa cin nasara ba.”
Hankali a tashe ya miƙawa Haroon jaridar tare da cewa.
“Ya Haroon gani zancen banzan da aka rubuta kan hotunan Hamma.”
Da sauri Haroon dake sauƙowa kan stpes ɗin sauƙowa falon daga dinning area,
ya ƙaraso. Hannuyasa ya amshi jaridar.
Wani irin azabebben zufane ya fara keto mishin ganin abinda aka rubuta a jikin jaridar.

Jin jikinshi na rawane ya sashi zama kusa da Sulaiman.

Ummi kuwa dake tsaye a dinning area tana haɗawa.
Jafar abin da zaici, gaba ɗaya ido ta zubo musu cikin taraddadin me aka rubuta.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu wata iriyar shaƙiyiyar dariya tayi tare da cewa.
“Ya haka dai ƴan kanzagi, ku bawa shi uban gidan naku, jaridar yage me aka rubuta, daga nan sai inga bakinshi da baya mutuwa da bada amsa ko zai iya cewa wani abu.”
Baba Nasiru da Baba Basiru, ma fuska cike da farin ciki suka zauna.
Laminu kuwa miƙewa tsaye yayi tsakiyar faffaɗan falon cikin ɗaga sauti yace.
“To tunda bazaka iya bashi ba, bani ni in karanta mishi.”
Yana ƙarishe mgnar yasa hannunshi ya amshi jaridar.
Cikin ɗaga sauti ya fara karanta rubutun dake rubuce a ƙasan hoton da gefe da gefenshi.

“Abun kunya, ya baiyana jikan sarki Nuruddeen Bubayero ɗaga Habibullah,
Yayiwa ɗiyar Fulani fyaɗen da yasa.
Hanun Sarki Lamiɗo ya kama hannun Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero wanda yake limamin masalacin ƙofar sarki ya miƙa shi ga hukumar addini musulunci.
Gashi anayi mishi bulalin haddi kamar dai yadda Musulunci ya wajabta.

Wani irin murmushi Jabeer yayi, hannunshi yasa ya shafa tattausan gemunshi.
Cikin rashin karaya ya kalli Haroon cikin nitsuwa yace.
“Ɗan wannan abun ne kuke zaton zai kashe wannan bakin nawa da yake rayuwa da ambaton Allah!?
Shin ko kun mance tsawon shekaru da dama ana fataucin rufe bakin Ya Jafar, shima har yau baku samu nasarar hanashi ambaton Allah ba,
Duk sharrinku ya zame mushi al’khairi, tunda baya wani motsi ba tare daya kira sunan Allah ba, ikirarin ku na ya zauce, ya tabbata kune zautattun”.
Sai kuma ya ɗan kalli Gimbiya Saudatu, murmusawa yayi tare da cewa.
“Baki nafa bazai mutuba sai in nufashina ya bar jikina, batun shiga ɗakin sirri kuma, nifa wannan abin da kuketa haƙilo a kai ba wani baƙon abun bane a wurina.
sarauta a cikin jin jikina yake.”
Sai ya kuma juyo ya kalli Haroon da jikinsa yayi la’asar da lamarin su, miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Haroon wai ɗan wannan makircin nasune ya kashema jiki.
To kontar da hankalinka. Ni nan Muhammad Jabeer ƙi gudune sa gudu.
Tun kan suyi tunanin yin abu a kaina na nazarci abun.”
Juyowa yayi ya kalli Baba Nasiru cikin tsareshi da ido yace.
“Kaje duk inda ake saida jarudu ka bada farashin one million akan ko wanne jarida kaga in za’a fito maka da wannan jaridar, in bada wannan ƙwaya ɗayar kaga dai itama kuma gata a gabana.”
Cikin tarin mamaki suka zuba mishi ido.
Shi kuwa gaban Laminu ya isa cikin isa ya miƙa mishi hannunshi tare da cewa.
“Bani shi nan”.
Cikin tsananin tsoro da firgici ƙarara. Jiki na rawa Laminu ya miƙa mishi. Sabida kwarjin Jabeer ya mishi nauyi a idonshi ya kuma san artabu dashi ba daɗi.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu wani murmushi tayi mai cike da taraddadi da al’hini da nazarin yadda zataga bayan wannan yaron mai bakin tsiya.
Jaridar gabanta ta miƙa mishi.
Kanshi ya girgiza tare da kaɗa mata yatsarshi manuniya cikin rashin tsoro da ƙasaita yace.
“Ba kifa kai matsayin da zaki nuna min wani abin da idanuna basu rigaya sun ganiba ko basu san dashiba domin ke a makance kike rayuwarki, Ni kuwa nan da kike gani idona buɗe suke ras.
Ita wannan itace tayi bayanin abinda ya faru na gsky a Rugar itace tai bayanin cewa bulalin shaɗi akayi min bana Haddiba to sai me kuma!?”.
Shiru sukayi gaba ɗayansu.
Kowa da abinda yake nazarta a ranshi sai bugawar da zuciyoyinsu keyi.
Buɗa al’kyabbar jikinshi yayi tare da kuma haɗe ta cikin fillanci yace.
“In kun gama ihun ku ficemin daga Side ɗina Dan ba haɗamu akayi ba. Kuma ku sani (MOH ALLAH WUJI FURƊATA).”
Yana faɗin haka ya juya ya nufi falonshi.

Ita kam Gimbiya Saudatu ta cika tayi maƙil.
Baba Nasiru da Baba Basiru kuwa,
A kufule suma suka fita.
Haroon kuwa ido ya zuba musu.
Barrister Kamal kuwa murmushi yayi mai tarin ma’anoni kana shima ya fita Sulaiman na biye dashi.

A hanyarsu ta komawa side ɗinsu ne, Gimbiya Saudatu ta kalli Laminu cikin takaici tace
“Banza kawai me tsoron zuci me dan ya matso kusa dakaii ka wani firgita ka razana har ɓari jikinka keyi ka miƙa mishi jaridar, da zamu iya kaita a tallata”.
Wani irin wawan ajiyan zuciya Laminu yayi tare da cewa.
“Uhummmm Umma kenan wato, fa duk wannan kumfar bakin da kikeyi abinda yasa kike yinta da jin daɗin yinta, dan wancan Jabeer ɗin bai taɓa kifa miki bari bane shiyasa.
Wallahi Allah da ya taɓa marinki da waɗannan hannayenshi da kike ganin taushinsu kamar na jarirai shakka babu, wlh suma zakiyi sai an yayyafa miki ruwa”.
Cikin kufula Baba Basiru yace.
“Kai tafi daga nan banza mai zuciyar mata, ji abinda kake cewa kan mari ɗaya tak daya taɓa yi maka”.
Wani irin kallo Laminu yayi musu kab lokacin da suka shiga falon Gimbiya Saudatu.
Cikin rumtse idonshi sabida tuno marin da Jabeer ya kifa mishi randa yayi gangancin zai zageshi.
Da sauri ya buɗe idanunshi cikin kara yace.
“Yesss sabida baku ya shararawa mari ɗayanba shiyasa.
Kuna sanefa mari ɗayan da yayi min. A take kunnena ya rinƙa zubda jinin da Ni dai har yau bansan ta inda ya ɓulɓuloba, wlh Allah lokacin daya mareni kusan suma nayi, har yau in na tuno marin sai inji kunnena yayi gummmmm”.
Cikin zafi Gimbiya Saudatu ta yunƙuro zata surfawa ɗan nata masifa, sai ta kuma komawa ta zauna jin Baba Nasiru na cewa.
“Uhummm Dafa gskyar Laminu, in dai Jabeer ya ɗauki hannun mahaifinshi to tabbas, suna da zafin hannu mai ban tsoro,
In dai ya gado hannun Ya Habibullah to fa duk abinda suka mara wlh in dai dabbace sai dai a matso mata da wuƙa, in kuwa mutum ne to, tabbas zai sha azaba mai raraɗi.
In jifa ne ma sukayi ma basa saɓawa saiti sai sun samu abin harinsu, in kuma tsuntsune ko ƙananan halittu tofa in suka harba sai lahira.”
Sai kuma ya ɗan tsaya ya kallesu cikin dakiya yace.
“Munada buƙatar sabon shiri, akanshi, zamuyi mgnin bakinshin nan da baya mutuwa”.
Cikin takaici Gimbiya Saudatu tace.
“A duk cikin ababen da ake dangantawa dasu babu, abinda yafi cimin rai kamar meda, zoo ɗin masarautar sade ɗin Jabeer.
Wlh duk sanda najiyo kukan Ɗawisun Masarautar da sauran tsuntsaye nakiji kamar in je in samisu shinkafar tsuntsaye suci su mace kab ɗinsu kowa ma ya huta.”
Barrister Kamal dne dake,
Jinsu ta window ɗin falon.
Ya jinjina kai tare da jan hannun Sulaiman suka tafi yana mai cewa.
“Uhum naku burin dai baza taɓa cikaba in sha Allah”.
Su kuwa nan sukaci gaba da tattaunawa yadda shirunsu a kanshi zai kaya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button