GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Su kuwa su Jalal zama sukayi suna kallon Ishma da Junainah daketa sabgoginsu.

A hankali Sheykh ya zauna tare da kallon Jamil dake zaune tsakiyarsu Giɗi a hankali yace.
“Ka barsu su huta mana”.
Cikin sanyi Jamil yace.
“Allah ko Hamma Jabeer ina so in tafi wurin Khadijah ma sai inji zuciyata na tsinkewa kamar dai zan samu wani abu”.
Cikin kula Sheykh yace.
“Uhmm duk haka mukeyi kaita mai-maita innalillahi wa innailaihi rajiun”.
To yace.
Shi kuwa Sheykh nitse ya kalli Gaini da zai kai sa’an Affan.
Cikin kula yace.
“Sannunku da hanya”.
A tare sukace sannu.

Jamil ne ya ɗan kallesu tare da cewa.
“Shine babban yayanmu Sheykh da yasa aka fito daku”.
Da sauri suka ɗan gyara zama suka matsoshi tare da cewa.
“Allah sarki bawan Allah mun gode Matuƙa Allah ya saka da al’khairi ya kula da ahlinka fiye da yadda ka kula damu”.
Cikin jin daɗi yace.
“Amin ya rabbil izzati, amman kuma duk haka ya farune sanadin Sulaiman da aka rufeshi tare daku”.
Cikin gamsuwa sakace.
“Ayyah”.
Sai kuma Giɗi ya ɗan share hawayen da suka zubo mishi tare da cewa.
“Ayyah bawan Allah yaushe zamu koma Rugar Bani muga Bappa da Inna da Ummey da Shatu da Junnu”.
Cikin gamsuwa da tausayinsu Sheykh yace.
“In sha Allah nan kusa amman nafi son sai naga kunyi aski kun ƙara hutawa, gobe zuwa jibi da kaina zan medaku”.
Cikin wani irin masifeffen jin daɗi sukace.
“Allah ya kaimu”.
“Amin Amin”. Yace kana ya musu sai da safe.

Daga nan wurin Abbanshi da Lamiɗo da Galadima yaje suka ɗan yi wata mgnar kana ya dawo.

Ranar dai haka suka kwana gaba dayansu babu wanda yayi isasshen bacci sabida masifar bugawa da ƙirazansu keyi.

A can Rugar Bani kuwa.
Ko abincin dare Ummey bata iya ciba.
Haka nan sai taji zuciyarta na tsinkewa yana bugawa.
Tun abun bai damunta har ta gayawa Bappa, so ya bata ƙarfin guiwa da yin addu’a.

                 *Ba'ana*

Zaune yake gaban yaransa cikin rauni da yanayin damuwa yace.
“Nanda wata uku masu zuwa zan koma ƙasar Nigeria zanyi yaƙin neman Shatu koda zan rasa rainane, zan koma gareta.
Zan gaya mata ko mutuwa nayi sonta ne ajali na”.
Cikin bashi ƙarfin guiwa ɗaya daga cikinsu yace.
“Zama kayi nasara”.
A hankali yace.
“Babu tabbas, domin tunda na rasa Shatu nakega nayi rashin babbar nasara”.
Sai kuma ya miƙe ya shiga cikin ƴar ƙaramar bukkarsa.

Murmushi Baron yayi tare da katse kiran da yayi Sheykh yana jin duk bayanan Ba’ana.
Dan shi Baroon yanzu ya zama ɗan aikin Sheykh dan tun zuwansa lokacin ciwon hannun Shatu.
Da fari har yasa a kirasa daga baya yasa aka dawo dashi.
Ya biyashi kuɗi masu tarin yawa, yayi mishi duk bayanin ɗaya nema, kana yasashi ya koma wurin Ba’ana kuma ya naɗo mishi rahoto da duk wani motsin Ba’ana yana turo mishi.
Alhamdulillah kuma yanzu duk shirin kama Ba’ana yakeyi.

Washe gari ranar asabar yau babu aiki.
Da misalin ƙarfe goma na safe jirginsu Abboi ya sauƙa cikin birnin Ɓadamaya.

Kai tsaye Salmanu yayi musu jagora zuwa Rugar Bani dan a take suna sauƙa wasu tsala-tsalan motoci guda biyar suka iso wanda dama su tun jiya suka iso.
A ƙasan plate number motocin akwai tambarin hatimin kan shanu a ƙasa ansa Abboi, irin tambarin dake jikin jiragen Abboi kenan.

Suna zuwa kuwa babu ɓata lokacin suka isa har cikin gida.
Inda nan Arɗo Bani da kanshi da sauran dattawan sukazo.
Bayan sun gaggaisane Abboi ya ɗan yi gyaran murya tare da cewa.
“Toh Alhamdulillah lallai komai yayi forko to tabbas yana da ƙarshe, to bayan bincike da bin diddigi dai mun gama fahimtar inane asalin wannan baiwar Allah’n kuma munada yaƙinin daga masararutar Joɗa ta fito.
To yau dai kam ranar data kamata mu shiga da ita ciki da yardar ubangiji tazo.
Kamar yadda muka tsara, yanzu zamu tafi”.
Cikin tsananin jin daɗi da kuma fargabar ko ya al’amarin zai kasance Bappa yace.
“Alhamdulillah mu duk a shirye muke, fatanmu Allah yasa ina munje ta tuna baya, ta tuno ita wacece”.
Da sauri Arɗo Bani yace.
“In Sha Allah ma zata tuna Malam Babayo”.
“Allah yasa haka”.
Al’ameen ya faɗa.
Amin Amin sukace kana duk suka miƙe suka fito.

Kana Bappa yazo yacewa Ummey da Dedde su fito.
Nan suka mara musu baya.

Mota ɗaya Bappa da Abboi da Arɗo Bani suka shiga.
Ummey da Dadde da Al’ameen kuwa suma mota ɗaya suka shiga.
Sauran kuma ƴan tsaronsu ne a ciki sai motar Yah Salmanu da Hafsi ƙanwar Shatu a haka suka fito daga Rugar Bani suka nufi Masarautar Joɗa.

A hankali Ummey ta jingine kanta da jikin kujera tare da dafe ƙahon zuciyarta a hankali ta furta innalillahi wa innailaihi rajiun”.
Sabida tsananin tsinkewar da zuciyarta keyi Dedde kuwa hankalinta naga makiyayan dake zirya.

A nan cikin birnin Ɓadamaya a tsakiyar Masarautar Joɗa kuwa.

Gaba ɗaya su Umaymah suna falon Shatu.
Aunty Rahma ce da su Sara a kitchin, Aunty Juwairiyya tana part ɗinta da Hibba.

Junainah da Ishma kuwa suna kitchen tare da Aunty Rahma.
Kowa sabgar gabansa keyi.
A hankali Shatu ta miƙe ta nufi ƙofar falon Sheykh da sallama a bakinta.

Shiru ba kowa a falon tray’n breakfast ɗinshi shida Haroon ta ajiye bisa Dinning table.
Ganin ba kowane yasa ta turo kanta cikin bedroom ɗin.

Shiru ba kowa a hankali ta ƙara so ciki tana cewa.
“Salam Yah Sheykh”. Ƙofar bathroom ta matso a hankali ta tura ba kowa a ciki komai yana kimtse tsab-tsab.
“Toh ina yaje kuma yau Lahadi kuma ai babu inda zaije”.
Shiru tayi tare da juyowa ta matso tsakiyar ɗakin jujjuya kanta tayi ba mutun ba alaman mutun a ɗaki.
Har ta juya zata fita, sai kuma tayi sauri ta juyo tazo bakin gadonshi, abun data hanƙo ƙasan pillow’nshi ne yasa ta sunkuyowa da sauri hannunta tasa ta zaronshi.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun”.
Ta faɗa jiki na rawa tare da sakin fuskar robar da Sheykh ake amfani da ita a matsayin Jahan.
Da sauri ta juyo da nufin zata fita, sabida tsoron daya rufeta.
Sai kuma tayi sauri taja da baya tare da zare idanunta dai-dai lokacin da ta iso jikin marfin wodurob ɗin sa
Wanda yayi dai-dai da lokacin da Sheykh ya turo marfi ya fito.
A gigice take jujjuya kai tare da zaro ido.
Sai kuma ta juya da sauri ta kalli fuskarnar da ƙarfi ta buɗe baki tare da cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun Yah Sheykh”.
Da sauri yasa hannunshi ya kamo nata ya fizgota jikinshi cikin haɗe fuskarsu wuri ɗaya yace.
“Na’am Aysha please kada kiyi ihu tsaya nitsu nine Muhammad Jabeer Yah Sheykh mijinki Abu Afreen”.
Cikin yanayi kaɗuwa tace.
“Yah Sheykh kai mutum ne ko al’jan”.
Da sauri ya kamo hannunta suka iso gaba durowar.
Buɗe ƙofar yayi, kana a hankali yasa hannunshin ya ture, al’kyabbas ɗin shi dake jere a hanga a saƙale, sai ga wani ƙofa mai kamar glass.
A hankali yace.
“Aysha nitsu ki jini kinji ko”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Toh”.
Kanshi ya gyaɗa kana a hankali yace.
“Kinga wannan wurin ko?”.
Da sauri tace.
“Eh naga kamar ƙofa ne”.
Jawota yayi suka ɗan matso hannunshi yasa ya tura ƙofar da sauri tace.
“Lahh”.
Sabida ganin wata ƴar siririyar hanya mai tsawo.
A hankali yace.
“Ni mutum ne Aish yanayin tsarin masararutar Joɗa ne yasa dole nake amfani da wasu ababen.
Kinga wanan hanyar har cikin bedroom ɗin Lamiɗo da Abba na duk akwai su.
Muna haɗuwa dasu a ɗakin Lamiɗo lokuta da dama.
In kina so anjima zan nuna miki, dan yanzu Lamiɗo ya rufe ƙofarsa ne da yanzu zamuje”.
Da sauri tace.
“Me kukeyi a ɓoyen”.
Jawo ƙofar yayi ya rufe kana a hankali yace.
“Ina wani aikine Aish Kuma aikin sirrine, tsawon shekaru inayi babu wanda ya sani sai Lamiɗo da Abba na da Umaymah sai yau kuma da kika zama ta uku”.
Ya ƙarashe mgnar yana jawota suka zauna bakin gado.
A hankali ta sauƙe numfashi ido ta zuba mishi a hankali tace.
“Kai SS ne ko Yah Sheykh?”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Ba’a faɗa kiyi shiru kada wani yaji kinji ko sirri ne Boɗɗo na”.
Murmushi mai cike da jijjina tayi mishi.
Shi kuwa ruggume ta yayi ya koma baya ya kwanta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button