GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Kai tsaye sashin Gimbiya Aminatu ta wuce, ta sanar mata yadda sukayi da ɗan nata.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya miƙe al’kyabbar jikinshi ya zare, kana ya nufi bathroom da jallabiyar.

Yana shiga ya zare jallabiyar da snglet ɗin. Kana ya shiga wurin wonkan.
Ruwan sanyi ya sakarwa kanshi.
sabida sarawar da kanshi keyi,
tun ihun dasu Baba Basiru sukayi mishi a kanshi.
Ga kuma wani sabon zance na zagaye idanun mayu da kulullukan masu konciyar ɗaukan rai na masarautarsu.
A ƙalla yayi mituna biyar ruwan sanyin na zubo mishi a tsakiyar kai, kafin ya fara sauƙe ajiyan zuciya alamun kan ya fara lafawa.
Al’wala yayi kana ya fito.
A nan drower’n glass dake bathroom ɗin nashi ya kimtsa kanshi cikin wasu datsastsen yadi mai masifar kyau Super Nour, Noble blue mai ɗan karen kyau, tattausan yadine mara nauyi, kana yanada ɗan shara-shara kaɗan, riga da wonɗo ne dai-dai jikinshi rigar half jomfa ne wanda aka watsa mishi aiki da da baƙin surfani.
in ka tsura mishi ido sosai zaka iya hango shatin snglet and white boxes jikinshi.
Wani Oud mai daɗin gaske ya fesa.
Kana ya fito.

Baƙar fula ya kafa a kanshi wanda ya bawa tattausan gashin kanshi damar baiyana ta gefe da gefen kanshi da kuma ƙeyanshi.

Fararen kyawawan Ƙafafunshi, ya zura cikin. Wasu tattausan takalma baƙi.
Sai kuma yasa hannu ya ɗauki carbinshi.
Agogon dake liƙe saman mirror ya kalla,
Lokacin sallan la’asar yayi, dan haka dole babu baccin tsakanin azahar da la’asar ɗin da ya dawo yi.

A masallaci ya samu su Haroon da Jamil.

Bayan anyi sallan ne kowa ya kama sabgogin gabanshi.
Shi Jabeer komawa gida yayi.
Ya saka garen kayan jikinshin kana.
Ya fito, Ummi ya samu tsaye a tsakiyar falon, cikin kula tace.
“Zaka fitane?”. Kai ya gyaɗa mata alamar eh.
ba tare da damuwar rashin bata amsarba tace.
“Da yan rakiya ko kai ɗaya?”.
Yana gyara zaman hular kanshi yace.
“Ni kaɗai. Zanje gidan Malama Abubakar ne!”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ka gaida minshi”.
“In sha Allah zaiji. Umaymah fa?”.
Gane abinda yake nufine yasata cewa.
“Tana can sashin Gimbiya Aminatu, wurin ɗiyarta Amarya Aysha”.
Kanshi ya ɗan sunkuyar ba tare da yace mata komai ba,
ya fita.
Malam Abubakar shine, malamin da ya fara ɗiga mishi harafin Ba”un a allon shi, wato Be a fillance, Basinmi’arra a hausance ko?.
A wurin shi yayi sauƙan forko, sai dai zuwa yanzu, shi Jabeer shike ƙara wa Malam Abubakar sani, akan Nahawu da Tajwid sabida shi da karatun zaure yayi.

Umaymah kuwa, ita da kanta ta sanarwa Lamiɗo cewa, gobe Sheykh zai gabatar da amaryarshi.

Haka yasa, ta fara shirya Aysha, shiri na musamman.
Cikin Hadiman Juwairiyya ɗaya daga cikinsu.
Mai suna saratu, itace Umaymah tasa ta yarfawa Aysha zanen lalle mai ɗan karen kyau.
Kana Ummi da kanta ta wonke mata kai sabida ita keyiwa Juwairiyya ma.
Sosai ta fito ras.
Ita kuwa Shatu duk abinda sukeyi Mata.
Tunanin Hibba al’hinin da tun randa tazo bata kuma ganinta ba.
tana son ta tambayesu ta rasa ta ina zata fara, dole dai haka ta haƙura tai shiru.

Washe gari ranar talata. Da hantsi, ko ina na sashin Gimbiya Aminatu sai ƙashi yakeyi, sabida shiri da kimtsa amarya.
Umaymah da kanta take kimtsata, wani irin dakekken wagambarine mai matukar kyau Royal blue, tasaka doguwar rigace. Tayi cib-cib da jikinta.
wani irin ɗauri ɗan kwali Aunty Juwairiyya ta murza mata a kanta, irin mai stpes ɗin nan.
Kana sai wata farar al’kyabbar masarauta fara ƙal mai kolliyar zaren aiki da ulunta Royal blue.
da surkin Golding color mai sheƙi.
Wasu fararen takalma masu ratsin Sky blue ne a kekyawan kafarta da yasha jan lalle, takalman basu cika tsini da tuduba, sai dai kuma ba dab da ƙasa bane.
Tayi kyau iya kyau, sai ƙamshi da sheƙi take zubawa.
Umaymah ce ta kama hannunta har zuwa falon Lamiɗo, wanda bai rigaya ya fita fadaba.

Gefen Gimbiya Aminatu ta ajiyeta, kana tace.
“Bari inje inzo da Angon.”
Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
“To kuyi sauri dai”.
To tace kana ta fita.

A can sashin Sheykh Jabeer, kuwa.
Da alamun wonka ya fito, a nitse yake kimtsawa, cikin wani fitinenne yadi mai taushin gaske.
yadin Royal blue ne mai masifar kyau.
rigar half jomfa yar tsukekkiya,
tsaki ya ɗan ja lokacin daya gama dai-dai-ta zaman rigar a jikinshi sabida tayi kib-kib a jikinshi har kamar ta ɗan matseshi.
Wondon kuma irin mai iya kuibin sawune, irin sakun wondunan ahlul sunna.
a hankali ya iso gaban drower’n da hulunanshi da hirami da baƙin abun saman hiramin ke jere a ciki.
Har yasa hannunshi bisa wani farin hula, sai kuma ya sunkuya ya ɗan kalli. Kanshi.
Fuskarshi ya ɗan tsuke, sai kuma ya ɗan juyo jin muryar Haroon yana cewa.
“Wow masha Allah, gsky kayi kyau, Please ka fita haka mana, ka ganka ɗan saurayi mai jini a jika, amman in kasa al’kyabbar nan, sai kwarjininka yayi yawa yaseen.
Ni kaina sai inji ina shakkarka,”.
Kai ya ɗan shafa kana yasa hannunshi ya zaro hiraminshi fari da baƙin zagayen.
ɗaya marfin drower’n ya buɗe tare da zaro wata dakekkiyar al’kyabbar fara mai ratsin blue na zaren aiki gaba da bayanshi.
Gaban gado ya dawo yana warware al’kyabbar tare da cewa Haroon.
“In na fita a haka ai ji zanyi kamar babu tufafi a jikina, sabida sunyi min kaɗan.”
Ya ƙarishe mgnar yana zura al’kyabbar a jikinshi.
Masha Allah, Haroon yace.
Kana ya matsoshi yana tayashi gyara zaman al’kyabbar yana cewa.
“Duk shigar da kayi tana maka kyau, in na ganka ba al’kyabbar sai inga kamar kafi kyau.
In kuma kasa al’kyabbar sai inga kafi kyau”.
Baice dashi komaiba yaci gaba da gyara sakun hiraminshi,
saida ya gama dai-dai-ta hiramin sai ya juya ya nufi, wannan drower’n da hulunanshi ke jere a steps biyu na sama.
Biyu na ƙasan kuma jerin takalmanshi ne.

Fararen takalma masu taushi ya saka ƙirar Gucci,
Zara-zaran yatsunshi sarari sabida ba sau ciki bane ba kuma half cover bane.
turare ya fesa, tare da sa hannunshin ya shafa sajenshi.
Kana ya kalli Haroon daketa ɗaukar shi hoto.
Cikin tura baki Haroon yace.
“Na bari, nasan yanzu zakayi ƙorafi, yanzu ina zakaje?”.
Yana fita yace.
“Valli Hospital, akwai yaron da zan duba aikin da akayi mishi”.
Bayanshi ya biyo tare da cewa.
“To sai ka dawo”.
Ni zamuje wurin Budurwar Jamil taga babban yayanshi.
Wani kallo ya mushi tare da cewa.
“Allah ya shiryeka babban kobo”.
Dariya Haroon yayi tare da cewa.
“Eh naji na yarda, zanje yaro ya samu matsala da ita tanata wahal dashi ba dole inje in dai-dai-ta musu matsalar ba”.
Juyowa yayi jin abinda Haroon yace cikin sakin gajeren murmushi yace.
“Uhumm yaushe ka zama luwali, bani da lbri, to kai taka matsalarma yaushe ka warware ta, kun iya cikamu da zancen ku ƴan soyayya ne, kuma bakuma san yadda ake soyayya da magance matsalolin ta da tattalinta gudun ta lalaceba”.
Wani irin dariya mai sauti Haroon yayi tare sara mishi.
Da sauri ya juya, da nufin tafiya,
sai kuma yaga Umaymah na tsaye a gabanshi.
Hannunta tasa ta kamo nashi tare da janshi suka fara tafiya.
Cikin sanyi yace.
“Oh Umaymah ina zamuje?”.
Haroon kuwa baki ya taɓe tare da cewa.
“Wlh gobe zan koma in sha Allah, komai sai an nunawa mana ƴan ubanci”.
Dariya Umaymah tayi tare da cewa.
“Allah kiyaye hanya”.
Da sauri yace.
“To na fasa tafiya”.
Suna gab da fitane yace.
“Umaymah sakeni karmu fita a haka”.
Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa.
“To taho”.
To yace mata kana yabi bayanta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button