GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Zan ƙara roƙo ba domin irinku kangararruba a a sai dan masoyan Allah da Manzonsa, dan Allah kada ku fitarmin da littafina. In kin san kin sayane dan ki fitar min da littafina to dan Allah da Manzonsa kizo kimin mgn ta pc kice kawai GARKUWA bani kuɗina bazan iya saya ban fitarba, wlh Salim alim zan meda miki kuɗinki in biki da godiya, in kuma baki sayaba zaki saya dan ki fiddane dan Allah kada ki saya. Dan Allah in kin rigada kin saya kuma Please turo ac no ɗinki kawai kadama kiyi mgnar kamai a take zan meda miki kuɗinki in cireki in miki godiya????????

Lamiɗo da Galadima da Sarkin Shaɗi. Bisa alamu wata mgna mai mahimmanci suke tattaunawa.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Umaymah cikin kulawa yace.
“Khadijah lale da zuwa Masarautar Joɗa.”
Da sauri Umaymah ta ƙarasa gabansu, cikin ladab ta zauna gabanshi tare da duƙar da kai tace.
“Allah rene Barka da dare”.
Kanshi ya jinjina irin na sarakuna kana yace.
“Barka dai Khadijah kinzo lfy, ya Sarki Aliyu?”.
kakan Haroon kenan wanda ya haifi baban shi.
Cikin girmamawa tace. “Yana lfy yace yana gaidaka”.
Kanshi ya jinjina, kana ya ɗan kalli Jabeer dake danne-danne a wayarshi.
Ya hakimce ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.
Jakadiyarsu kuwa tayi shiru a gefe kusa dashi.
Galadima da Sarkin Shaɗi kuwa, murmushi sukeyi suna kallon Jabeer.

Gyaran murya Lamiɗo yayi kana cikin dattaku yaci gaba da cewa.
“Ina amsawa, ya kika samu jikin ɗan naki?”.
Cikin murmushi ta juyo ta kalli Jabeer kai ta rusunar ganin samfa hankalinshi baya kansu cikin yin ƙasa da murya tace.
“Alhamdulillah na samu jiki ya worke!”.
Galadima ne wanda yake ƙanine ga baban Lamiɗo ya amshi zan da cewa.
“To sai ki sanar mishi batun komawa Rugar Bani, dan ramuwa bisa cika ƙaidar..”.
Shiru yayi bai ƙarisaba jin muryar Jabeer yana cewa.
“Ƙa’idar Allah da Manzonsa ne da zai zama dole sai an cika, ba ƙa’idar wani zalumci da tozarcinba”.
Kanshi ya ɗan tanƙwara a wuyanshi.
Kana ya zamo kaɗan ya zauna gaban Umaymah cikin nuna rauninshi yace.
“Ayyah Umaymah kada kice min inje, Please Umaymah ki fahimci wannan abunfa al’adace ba addini ba, kuma abune da kai tsaye zamu iya ce mishi makaruhi in ma bamu haramtashi ba, ya za’ayi inje in sake tuɓe kayan jikina a gaban duniya wai dan in daki wani. Ni bana so.
Ba dai sune suka kainiba, suka kuma ce a dakeni, to dan me zasu buwayeni da sai munje na rama”.
Haɗe fuska Umaymah tayi cikin kafeshi da ido tace.
“Ni bana iya yiwa iyayena musu. Jabeer tabbas na sani al’adace ba addiniba, amman ka sani duk wani abun da zakaga ya faru a duniya to akwai dalilin faruwarshi, kada kace zaka tsananta bincike tabbas lokacin zai baiya mana dalilin.
Bana son gardama kawai kaje Dan ALLAH”.
Hannunshi yasa ya dafe kanshi,
kana yayi shiru Umaymah ta gama dashi da tace dan Allah, ya sani tabbas da a madadinsa Ayyah ɗin da yace forkon mgnar da ya mata da ya rigata cewa Dan Allah da shike nan yasan zatayi shiru.
Shi kuwa Lamiɗo murmushi yayi tare da kallon Umaymah cikin jin daɗi yace.
“Allah ya miki al’barka”.
Da sauri tace.
“Amin ya Allah”.
Galadima kuwa, murmushi yayi tare da jinjina kai.
Jakadiyarsu ma cikin jin daɗin tasirin mgnar Umaymah akan Jabeer take murmushi sabida ta sani.
Shi mutunne mai kaifi ɗaya, in yace eh tofa eh ɗince inko yace a a to a’ance.
Especially baya son duk wani abu da zaici karo da addininshi.
Kanshi ya jinjina Umaymah alamar shikenan idonshi yayi jazir alamun dole akasashi yin abinda baya so.
Kana ya kalli kakarsa dake murmushi tsuke fuskarsa yayi tare da cewa.
“Gimbiya Aminatu muje ki bani gashin da kikayiwa Lamiɗo”.
Cikin dariya Gimbiya Aminatu tace.
“Iye gashinsama zan baka?”.
Da ƙarfi yace.
“Eh shi zaki bani, ai in dukane kam ya iya zille kanshi ya turani.
Shine dan gashinsa zakice iye”.
Murmushi tayi tare da bin bayanshi,
ganin Lamiɗo na mata alamun taje ta bashin.

Nan sukaci gaba da hira, suna tattauna wasu mahimman al’amuran da sirrine garesu iya su biyar.
Wato Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, Umaymah, Jakadiyarsu.
Bayan su babu wanda suke yarda da sanin sirrin Jabeer.
A hakanma kuma a suɗinma akwai wani sirrin da babu wanda ya sanshi sai Lamiɗo da Umaymah.

Suna zuwa har falonta suka wuce.
Wani kekyawan akoshi mai masifar kyau ta ɗauko mishi.
Ta ajiye a gabanshi.
Inda yake zaune a ƙasa bisa carpet ya naɗe sawunshi.
fork ɗin dake saman fefeyin ya ɗauka.
Daddageggen gaseshen jan namane wanda yaji wuta ya gasu gashin tukunyar ƙasa yayi tiɓis.
Sai wani irin ƙamshi na musamman yakeyi,

A hankali yake sa Fork ɗin yana yagan tattausan tsokokin yana sawa a baki.
Ita kuma tana zaune gefenshi.
Tafashesshen madaran shanu mai ɗan ɗumi ta miƙa mishi a wata ƴar ƙwarya mai kyau.
Taune naman yayi tare da haɗiyewa kana cikin zuba mata ido yace.
“Dole sai na karɓa da hannun nane? Ki ajiye mana.
Da wanne hannun zan amsa tunda inacin abinci dana daman”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Dole sai ka amsa, bazan baka shi a ƙasa”.
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
“Allah ya nuna min ranar da za’a bar.
Wannan tsare-tsaren shamfi na masarautar Joɗa. Komai da ƙaida da yadda ake yinshi”.
Ita dai miƙa mishi ƙwaryar takeyi dole ya ajiye spoon ɗin yasa hannunshi ya amsa.

Nan suma sukaci gaba da hira.
Sai kusan sha ɗaya Umaymah da Jakadiyarsu suna fito.
A nan Gimbiya Aminatu ta ajiyesu suma saida sukaci gashin nata kafin suka tafi.

Kafin su isa Side ɗinsa dai sha biyun dare tayi.

Haka yasa suna isa suka samu ba kowa a falon.

Sai Haroon da suke jiyo muryar sa, a falon Jabeer.

Cikin nitsuwa ya matso kusa da Umaymah a hankali yace.
“Sai da safe Umaymah kiyi bacci ki huta.”
To tace har ta juya zata tafi sukaji Muryar Haroon yana cewa.
“Abba yazo wurinki zaku gaisa bai samekiba, nace mishi kun tafi wurin Lamiɗo yace, to saida safe ya gaidaki da hanya Hajia Mama ma yanzu ta fita, tace Lamiɗo ya riƙe mata ƙanwa”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“To Allah ya bamu al’khairi saida safen”.
Amin Amin suka ce.
Kana shida Haroon suka wuce Side ɗinsa.

It’s kuma Umaymah da Jakadiyarsu suka wuce.
Side ɗin da kullum in dai Umaymah tazo nan take sauƙa.

Suna shiga suka samu, tuni Hibba tayi bacci, wannane ya basu damar tattauna wasu mahimman sirrukansu.

Nisawa Umaymah tayi bayan ta saurari jawaban Jakadiyarsu Jabeer cikin tsantsar tafasar zuciya da tarin baƙin ciki tace.
“Uhummm suyi dai Ni nan ina dai-dai- da ƙugun ko wanne shege da shegiya,
In sha Allahu zasusha mamaki.
Zasuga yadda Ubangiji ke ikonsa, ban cire raina ƴar uwarta zata sake rayuwar enci da salama, da izinin Ubangiji zataga sakayar waɗanda suka cutar da ita da yaranta a gaban idonta.

Cikin zubda hawaye Jakidaya tace.
“In sha Allah, sai farin ciki ya dawo, a sashinta, inata addu’a a kullum a cikin dukkan sallolina, Allah ya kare ahlinta, ya kuma baiya gsky tayi halinta kowa ya gani”.

Amin Amin Umaymah tace tare da share hawayenta.

Washe gari ranar Alhamis. Ta kama yau kwana shida da faruwar gasar Shaɗi, kana gobene za’a koma dan ramuwa,
A goben kuma zai cika kwana goma da kisan gilla da kafurai ƙabulun Ɓachama sukawa Fulanin Rugar Bani.

Misalin ƙarfe sha biyu na safe.
Fadar Sarkin Nuruddeen Bubayero Joɗa, cike take maƙil da tawagarsa kama daga.
Galadima, Waziri, Wambai, Dan buram, Dan iya, Ɗan isa, Ɗan Kade, Sarkin fada, Sarkin yaƙi, Sarkin Dowaki, Sarkin Gabas, Sarkin Kudu, magayaƙi, Jarma uban doma, Makawa Ɗurɓi, Turaki, Da dai sauran members ɗin masarautar baki ɗayansu, an cika anyi maƙil.
Sallama na tsaye can bakin ƙofar shigowa.
Dogari kuma suna tsaye gefen hagu da daman Lamiɗo.
Suna rike da mafici sunayi mushi fifita, ɗanzagi kuma yana gefe,
Kana wasu fadawan duk suna gefen.
Gyaran murya Lamiɗo yayi tare da gyara zaman shi cikin shugarsa ta sarakuna masu al’farma, a hankali yace.
“To da farko dai fatan duk kowa na lfy”.
Da sauri Ɗanzagi yace.
“Sarki ya gaisu yana yi muku fatan alkhaiy”.
Sai ya kuma juyo ya kalli Lamiɗo tare da cewa.
“Godiya suke.”
Kanshi ya ɗan jingina da tattausar kujerarsa da masu son gadonta sunfi a ƙirga, cikin ƙasaita yace.
“Kamar dai yadda muka tattauna, kwanakin baya akan sarkin Garin Shikan,
to yanzu zan zantar da hukunci.
Sarkin aike na bada umarni kaje garin Shikan ka karɓo min sandar sarautar Shikan ka kawo min shi, yau ɗin nan.
Kaje da jagorancin Galadima, da Matawalle da Makawa, sai sarkin yaƙi”.
Da sauri duk suka runsunar da kayu kansu tare da cewa.
“An gama”.
Nan take kuwa suka miƙa suka tafi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button