
Shima Ado ya sallami nasa mai taxi ɗin.
Kana yabi bayansu tafiya kaɗan sukayi yaga wasu mutane a ƙalla su shida, sunbi bayansu duk suna cikin shigar sut.
Al’amin dake gefen Bappa ne ya miƙo wa ɗaya na kusa dashi hannu.
Wayar iPhone ƙirar wannan shekarar ya miƙa mishi.
Sai kuma system ɗinshi.
Daga nan kan tsaye sukaje suka shiga jirgi.
Dole Ado ya rakasu da ido.
Su kuma jirgi ya ɗaga dasu.
Tun kafin Ado ya koma gida ya kira Sheykh ya labarta mishi.
Murmushi Yayi jin abinda Ado yace mishi. Kai ya jinjina tare da danna wasu ababe a wayarsa.
” ?+? “.
Murmushi yayi kana ya jefa woyar a al’jihunsa.
Bai shiga gidaba sai bayan sallan isha’i.
Yana shiga kuwa ya samu su Ummi a falo.
Aysha da hannunta ya ɗan fara zogin.
ta bishi da ido.
ganin kamar bazata tashi bane yasa.
“Umaymah cewa tashi kije ya miki tofin.”
To tace kana ta miƙe, ta nufi Side ɗin nashi.
Babu kowa a falon sai dai ta hango shigarsa ɗakin.
A hankali tabi bayanshi tura ƙofar Bedroom tayi tare da sallama.
Kana ta kutsa kai cikin ɗakin.
A hankali ta isa tsakiyar ɗakin babu kowa.
cikin sanyi tace.
“Ina jiranka dan Allah kamin tofin”.
Shiru taji ba mgna ba kuma motsin komai a ɗakin.
Cikin sanyi ta ɗan fara hurawa hannunta iskan bakinta.
Tana kallon ƙofar Bathroom ɗin.
A hankali kuma ta miƙe tana cewa.
“Shyyyuuu hahjjyyyyyyyt”.
Sai kuma ta matso bakin ƙofar Bathroom ɗin da niyar ta bubbuga ƙofar.
Tana sa hannu bisa ƙofar ta buɗu.
Da sauri ta ɗan ja da baya.
A hankali tace.
“Yi haƙuri bansan a buɗe yakeba”.
Still ba mgn kuma ba motsin ruwa.
Hakane yasa ta ɗan leƙa.
Ganin ba kowane a ciki ta kutsa kai ciki tare da cewa.
“To ina kake ina ka shiga”.
Shiru wayam ba kowa, komai na bathroom ɗin yana nan fes-fes a kimtse.
Da sauri ta fito bedroom ɗin.
Waige-waige tayi ba kowa.
Haka yasa ta fito falon da sauri tana cewa.
“Umaymah ban ganshi bafa, kuma na hangoshi yana shiga ɗakin.
Na shiga kuma ban ganshiba.”
Ummi ce ta amshi zance da cewa.
“Ko ya shiga wonka ne”.
Da sauri tace.
“A a baya cikin bathroom”.
Umaymah ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
“Ki duba Dinning area ko yana can”.
Da sauri ta juya tana cewa.
“Ɗakin fa ya shiga, kuma ban ganshi ba.”
Ummi ce tace.
“To kije dai ki ƙara dubawa”.
Dube-duben tayi a falon kana ta koma cikin bedroom ɗin wayam fa
A hankali ta ƙarewa wodurob ɗin shi kallo, buɗesu tayi duka, tana cike da mamakin to ina ya shiga, dan tabbas taga shigarsa ya kuma za’ayi baya ciki to ina ya shiga?.
A haka duk ta bubbuɗe durowowin babushi babu alamarshi.
Falon ta sake fitowa tana mai jin zohin hannun yana tsananta.
Ɗaura hannun tayi a kanta tana jin idonta na kawo ruwa.
Umaymah ce ta shigo.
Ƙofar shiga cikin Garden ɗin su ta duba.
A rufe take babu alamun an taɓata ma.
Ƙofar ɗaya ɗakin ta nufa zata buɗe.
“Aysha tace.
“Allah ko Umaymah bai shiga nanba ɗauki shi ya shiga.
Kuma na duba baya ciki tako ina kuma banga fitanshi ba.”
“Ikon Allah to ina ya shiga?”.
Umaymah ta faɗa tana.
Shiga ɗakin. Jim kaɗan ta fito.
A gefe ta tsaya tana mamaki tabbas dai sunga ya wuce.
Da sauri suka miƙe ganin ya buɗe ƙofar ɗakinshi ya leƙo yana cewa.
“Umaymah lfy kuwa? Naji kunata salati”.
Da sauri tace.
“Kai muke nema bamu ganka ba, ina ka shiga Aysha tace baka cikin ɗakin.”
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta tare da cewa.
“Uhumm to dama ya za’ayi ta ganni tanata kuka ta gigita kanta ba dole ta makanceba”.
Cikin gamsuwa da hakan dan Umaymah ta yarda wata ƙil ciwone ya gigita Aysha shiyasa Bata ganshi ba.
Ita kuwa Aysha cikin zafin tace.
“Wlh Umaymah ba ciwo bane na duba ko ina ban ganshi ba”.
Kai Umaymah ta gyaɗa kana tace.
“To kije ya miƙi tofin”.
Miƙewa tayi ta nufi cikin ɗakin.
Ita kuma Umaymah ta koma falon.
Raɓawa gefe tayi ta shigo.
Shi kuwa maida ƙofar yayi tare da cewa.
“Zo nan”.
Matsowa tayi ya fara yi mata tofin
tana jingine da ƙofar yanayi yana hura mata iska.
A hankali ta fara lumshe ido,
ganin zatayi bacci ne yace.
“To jeki”.
Har zata fita sa kuma ya ɗan sha gabanta ido ya zuba mata kana a hankali yace.
“Ke komai kika gani sai kinyi mgn ne?”.
Kai ya jujjuya alamun a a.
Gashin girarta ya zubawa ido tare da cewa.
“Bubbuga Rumbun Abboi”.
Baki ta ɗan tura tare da cewa.
“Ni dai ba bubbuga Rumbun bace”.
Matsota ya farayi ganin hakane ta ɗan ja da baya ta jingina da ƙofar, kusa da ita ya kuma matsowa kana a hankali yace.
“To ke meyece in ba bubbuga Rumbun ba, ko kunya babu kin zauna gaban wanda ba mijinkiba, yana baki abinci har baki”.
Gashin tattausan gemshi ta ɗan kalla tare da cewa.
“To nida Yayana ɗan uwana, tunda mai bani Allah ya kawoshi ai sai ya bani kada yunwa ta kasheni”.
Murmushi mai sanyi yayi sabida tambaya ɗaya ya mata cikin amsa tambaya ɗayan kuma ta amsa mishi tarin tambayoyinshi. iskar bakinshi ya ɗan hura mata tare da cewa.
“Kince in baki ban baki bane?”.
Da sauri tace.
“Toh sai nace ne?”.
Ƙara matsowa kusa da ita yayi tare da ɗada mata girarshi ɗaya a hankali yace.
“Na’am sai kin ce mana shima ai ce masa kikayi ya bakin”.
Mutsu-mutsu ta farayi jin ƙirjjinshi na danne nata a hankali tace.
“Toh ai shi ɗan uwanane”.
Ba zato yaji mgnar ta subce mishi.
“Toh ai Ni kuma mijinki ne”.
Sai kuma yayi sauri ya matsa, tare da juya mata baya.
Ita kuwa sumar ƙeyarshi ta zuba ido kana a hankali ta juya.
Cikin lumshe ido ta fita.
Shi kuwa Sheykh wata iriyar sassayar ajiyar zuciya ya sauƙe mai nauyi.
Kana ys cire kayan jikinshi.
Sannan ya shiga wonka.
Bayan ya fitone yayi shirin baccinsa.
Kana ya kwanta.
Ita kuwa Aysha tana shiga ɗakinta ta kwanta sai bacci.
Umaymah kuwa na ɗakin Ummi suna tattauna wata mahimmiyae mgna,
sai ƙarfe sha biyu ta shigo.
Tayi mamakin ganin Aysha konce tana baccin.
A hankali tace, uhum tana tashi zan kai maka ita tunda ka iya kora masu maganin ka kora sarkin bakan masarautar Joɗa kana ka kora wanda iyayenta suka zo dashi.
Daga nan taje tayi al’wala tazo ta kwanta.
A can wani yankin kuma.
Sarkin baka ne da Ɗalhatu mai sa tayis ne,
zaune su, suna musu bayanin duk abinda ya faru.
Dariya tayi mai cike da jin daɗi tace.
“Uhumm ai zanyi maganin ƴan iska watan cin uwarsune ya kama.
Wannan shegen yaro Jabeer Allah ya sani bana ko son ganin fuskarshi.
Duk sanda na ganshi sai inji zuciyata ta tsinke hankalina ya tashi.
Ɗaya dake gefenta ne, yace.
“Aini da inada dama da a daran nan zan kashe shegu gaba ɗayansu.”
Kai ta juya tare da cewa.
“Uhum baka san rashin kunya da tijara da magangun da wannan matar tashi mai kama da aljana tayi minba ne.
Shiyasa dole in taka mata birki zanci uwarta zata gane bata da wayo.”
Daya na gefenta ne yace.
“Uhummm ni wlh da zan samu wutan zan bunkawa shegu duk su babbake”.
Nan dai sukaci gaba da yiwa Ahlin Sheykh tanadin mugunta.
A can cikin dajin kuwa zaune yake gaban bokanshi shi.
Cikin hatsala yace.
“Kace min abubuwa suna gabda nasara amman akwai tsaiko menene tsaikon gaya min shi in kaudashi”.
Dariya bokan yayi tare da zazzare idanu kana yace.
“To ka dai san babban abunda ya hanamu nasara kan yaron nan, shine addu’o’in da yakeyi da yawan zama da al’wala da karatun al’ƙur’ani.
To yanzu kuma na gano wannan matar tashi da aka aura mishi idonta a buɗe suke.
“Akwai makaran gado, wanda sukeda ƙarfin iko, ko jiya wata cikinsu tazo tajamin kunnen kada in kuskura in cutar da ita.
Sannan kuma akwai saurayi ta da ya raineta ya shirya mata jiki, kana tana iya gane sihiri a wuri duk ƙanƙantarshi.
To in dai ba rabashi mukayi da itaba ko a kasheta ba tsira zamuyi ba.
Kuma tana iya tona asirin kowa”.
Cikin tashin hankali yace.
“Uhumm zata kuwa bar Masarautar Joɗa nan kusa.
In kuwa ta nuna taurin kai tabbas zata bar duniyar nanda bada jimawa ba, bazan bar duk wani abun da zai shiga tsakanina da sarautar masarautar Joɗa ba”.
Daga nan sukaci gaba da tattaunawarsu.