
Affan, da Jamil kuwa murmushi sukeyi, Jalal kuwa ido ya zuba musu.
Hajia Mama kuwa sai wani irin sihirtaccen Murmushi takeyi wanda ita kaɗai tasan ma’anarsa.
Shi kuwa Sheykh ƙara matsota yayi da kyau har kamar zai ruggumeta, hannunshi na dama yasa ƙasan haɓarta ya tallaɓeshi tare da cewa.
“Aish! Ais.. da sauri ya ida ƙarasowa gareta lokacin da ya ɗago kanta yayi dai-dai da ƙaƙƙafewar da idanunta sukayi, kana numfashinta ya tafi cak ya ɗauke ta sum…!
Kiyi haƙuri da typing errors banyi editing ba, abubuwa sunmin yawa.
By
*GARKUWAR FULANI*
[3/16, 11:10 AM] +234 806 559 0880: Luuuh ida nunta suka limshe ta sume.
Da sauri yasa hannunsa ya tallabo ta faɗa jikinsa, cike da tsoro Ummi ta matsoshi tare da cewa.
“Sheykh lfy kuwa meke faruwa?”.
Cicciɓota yayi ya ruggumeta tsam a jikinshi kana, ya juya ya fara taku, yana ratsawa gefe.
Cikin tsananin tsoro Umaymah, Ummi, Mamma. Suka rufa mishi baya.
Yayinda Aunty Rahma kuwa da sauran tawagar ƙawayen Umaymah suke zaton, kawai wani salone hakan sabida abu da Ustazu sai kallo.
Hajia Mama kuwa da ido ta bisu tare da yin wani ɓoyeyyen murmushi mai cike da manufofi masu ƙarfi.
MC kuwa wani sassanyan ƙiɗan da DJ ya saki yake takawa rawa.
Yanayi musu kirari, Affan da Jamil kuwa tafi sukeyi tare da alamun, jinjina dan babu wanda ya gano Aysha a tsume take ko Haroon da Ibrahim da Jannart basu ganeba.
Da sauri Jalal ya miƙe shima ya rufa musu baya.
Da sauri Ummi ke biye dashi a baya tare da cewa.
“Sheykh lfy kuwa”.
A hankali ya jujjuya kanshi tare da cewa.
“Ummi a sume take fa”.
“Subahanallahi!”. Suka faɗa a tare.
Da sauri Umaymah tayi gabansu tare da cewa.
“Zo nan zo muje part ɗin Abban Haroon.”
Binta a baya yayi sabida yasan canne kaɗai zasu samu babu taron mutane.
Suna shiga part ɗin ta juya gefen da.
Wani ɗan madaidaicin Side ne mai kyau.
Wanda yake da ƴar tazara tsakaninsa da Side ɗin Abbansu Haroon.
Hannu tasa ta tura ƙofar.
Cikin wani ƙawataccen falo suka shiga,
da sauri ya kontar da ita bisa kujera.
Kana ya miƙe tsaye tare da sauƙe numfashi yana ɗan miƙar da hannunsa,
cikin ruɗani Mamma tace.
“Umaymah ya haka, bata da lfy tana sume kuma mu zauna da ita a gida mu tafi asibiti mana”.
Ta ƙare zancen a firgice sabida bata san matsalar Aysha ba.
Ummi ce ta ɗan sauƙe numfashi tare da cewa.
“To meya tayar da jikinta kuma lokaci ɗaya haka”.
Cikin takaici ya ɗan tauni lip ɗin shi na ƙasa tare da cewa.
“Uhummm to Ummi kuma kun sani mutun tana na nan matsala, sannan anzo ansa ƙiɗe-ƙiɗe ga ƙarin al’gaita, sannan kuma aka ƙara da sarewa.
Ko wanda baida komai a kan shi sai yaji tsikar jikinai na tashi.
To ga irinta nan, in kuma ba’a katse sarewar nanba duk zasuyi ta sumewa masu makaran”.
Cikin sanyi Umaymah tace.
“Wlh duk tsiyar Rahma ce, yanzu kayi wani abu ta farfaɗo yafi”.
Kanshi ya gyaɗa kana yace.
“Da fari aje ace subar wannan bushe-bushen sarewa da kiɗan tambarin, a ma tashi kawai a taron haka ya isa haka kowa yaje yayi al’wala magriba ta gabato.”
Jalal dake tsaye bakin ƙofar ne yace.
“To bari inje in gaya musu”.
Da sauri Ya juya ya fita.
Ita kuwa Ummi a hankali ta matso kusa da Umaymah kana tace.
“Muje kawai, ba komai zai kula da komai”.
To Umaymah tace jiki a mace, hankali a tashe, Mamma tace.
“Haka za’a barta”.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Mamma kana a hankali ya ce.
“Ba komai Mamma kada ki damu zata dawo dai-dai, kije kuyi salla”.
Bisa dole dai tabi bayansu suka fita.
A can wurin kuwa kai tsaye wurin MC Jalal yaje yace.
A tashi taron haka lokacin salla yayi.
Dole aka tashi kowa ya kama gabansa, bayan ƙannnen ango su Hibba sunyi liƙinsu.
Su Umaymah kuwa wurin suka koma taje ta jagoranci ƙawayenta suka koma cikin Part ɗinta.
Ƴan cikin garin Tsinako duk suka koma gidajensu sai ƴan nesa-nesa wanda duk gobe zasu tattafi.
Su Ya Hisham da Affan kuwa tare da Haroon da Ibrahim suka koma part ɗin da aka sauƙesu,
nan kowa ya fara shirin al’wala dan lokacin ya ƙara to.
Sheykh kuwa a can Side ɗin.
Su Umaymah na fita, ya maida ƙofar ya rufe, kana ya dawo gaban kujerar da ya kwantar da ita.
Tayi lib kamar gawa.
A hankali ya sunkuyo hannunshi yasa ya dafe hannun kujerar da kanta yake kai.
A hankali ya sunkuyo kanta sosai,
yatsunsa yasa tsakiyar goshinta ya ɗan buga da ƙarfi tare da cewa.
“BISMILLAH”. Kana yaci gaba da ɗan buge goshin nata, a hankali tayi wani irin sassanyan miƙa tamkar wahainiya, fatan idonta ta fara motsawa shi kuwa Sheykh ci gaba yayi da buge goshin nata tare da cewa.
“Aeeyshah! Aeeyshah!!.”
Cikin fizgar numfashin da mgn tace.
“Na’am”.
Haɗe fuska yayi tare da cewa.
“Ba ke na kiraba,”.
Da sauri tace.
“Ni ka kira mana kanata dukana a goshin da amton sunan Allah”.
Fuskarshi ya tsuke tare da cewa.
“Goshinki ko goshin matata! sanina dake kince kin tafi, meya kuma kawoki me kike nema?”.
Kwaɓe fuska tayi murya na rawa hawaye na zuba tace.
“Kirana ankayi tunda anka kunna Sarewa da al’gaita dole du inda nake zan taho”.
Cikin faɗa yace.
“Ke tafi daga nan maƙaryaciyar banza”.
A hankali ta buɗe baki alamun zatayi atishawa cikin tsawa yace.
“Tsaya ban gama mgn da keba in kika kuskura kika tafi, to tabbas zan jawoki in kuma ɗaureki in ƙonaki”.
Cikin rawar murya tace.
“Na tsaya, kayi haƙuri”.
“Maza tashi ki zauna”. Yace a faɗace.
Da sauri ta tashi ta zauna,
Gefenta ya zauna kana ya kamo hannunta ya riƙe gam saida tayi ƙara sannan yace.
“Baki san gidan da take bane”.
Da sauri tace.
“Na sani”.
“To ina take?”. Ya kuma tambayarta.
“Masarautar Joɗa take”.
Kanshi ya gyaɗa sannan yace.
“Na’am kin san kuma dole duk wanda ke cikin masarautar Joɗa sai yaji kakaki da al’gaita da tambura da sarewa tunda mabusar masarauta ne, ko kina nufin duk sanda taji sai kinzo kin fiddata cikin haiyacinta kin tozarta min aurena a bainal jama’a, in bana kusa ta faɗi har ƙasa a sume ko me kike nufi ace matata tana sume a kwance ƙasa”.
Da sauri tace.
“A a baza’ayi hakaba in sha Allah bazan zoba, in dai dan kiɗane da sarewa nayima al’ƙawarin bazan zoba, na dena zuwa har abadan dan Allah sake min hannuna”.
Kanshi ya jinjina kana yaci gaba da matse hannun da kuma karantar Baƙara da yakeyi a hankali.
Cikin kuka tace.
“Dan Allah kada ka cutar dani wlh nima ban taɓa cutar da Shatu ba, Ni makariyace a wurinta, dan Allah kada ka ƙonani, zan tafi dama ko iyayenta basu san in jikinta ba, sai dai sukayi zaton akwai wani abu jikinta tunda sa’i zuwa lokacin takan ga abinda bani adam basa iya gani da yardar ubangiji”.
Cikin sanyi yace.
“Wato dan raini baki taɓa baiyana a jikinta iyayenta suka saniba sai Ni Muhammad kikewa hakan ko?”.
Da sauri tace.
“Wallahi Allah kenan na baiyana a jikinta ne bisa dole da kuma ceton lafiyarta da kuma bata kariya dama kai kanka”.
Cikin hatsala yace.
“Ubangijina shine mai bani kariya, in kika kuskura na ƙara ji ko ganinki to tabbas zan babbakaki, fice min daga jikin mata dan kan babarki”.
Ai kuwa a take Aysha ta fesa wasu tagwayen atishawa guda uku.
Sai gashi ta koma ta konta lib a jikinshi tayi bacci.
Kanta dake bisa kafaɗarshi ya dungure tare da cewa.
“Jiki duk al’janu sai son bidi’a da sakalcin yin addu’a ma wai kin gajiya, gaba barinsu zanyi su mummurƙusheki zaki gane kurenki, wai Yah Sheykh na gaji kayi min addu’ar”.
Sai kuma yayi murmushi tuno jiya-jiya nan taketa mitar ya dena ce mata mai al’janu, wai harda cewa yana bazata a gari.