GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Tuni ita kam Allah ya mata rasuwa mahaifiyar Sittin kenan, yanzu mahaifinta ne kadai a raye, sai kuma ƙanninta da yake matsayin ɗaya daga cikin manyan limaman harami a yanzu sai sauran zuriyarta da yayu da kannenta.
Kowa na ahlinsu yasan Sheykh domin Sitti tana yawan zuwa dashi tun yana ƙarami, kana tana zuwa da sauran ma baki ɗaya, to shi Jabeer anan ƙasar saudia ya haɗa digiri ɗinshi na forko dana biyu. Shiyasa ya zama duk zuriyar an sanshi farin sani, ga kuma tarin kama da yakeyi da mutanen zuriyar wanda da zaran ka ganshi kasan jininsu ne.

Tafiya mai tsowo sukeyi cikin sararin samaniya suna keta gajumare, a ƙalla tsawon aha huɗu kenan suna tafiya.
Kafin suka sauƙa cikin babban Airport ɗin jidda, wanda yake tamkar zai fashe da jirage, ko wacce ƙasa ta duniya tanada jirginta cikin wannan babban Airport ɗin, tashin jirage da hawa da sauƙansu tamkar babu wani abun hawa a duniya sai jirgi.

Koda suka fito daga jirgin, wani jirgine na musamman suka shiga wanda yake daga fadar Mai Alfarma masarautar garin. Wanda ya turo a tarɓi ƴar uwar abokinshi da mahaifinsu keta begen gani.
A take suka shiga jirgin ya wuce dasu, asalin cikin garin makka, wanda pilot ɗin kuma ɗane ga Umaymah ƙanwar Mamansu Sheykh wato shima jikan Sitti ne ɗan Umaymah sai kuma Jannart wacce ta biyo Haroon Dan tarban kakar tasu wacce ita kuma ƴace ga babban ɗan Sitti wato ƙanwar Juwairiyya ce kuma anan take karatu.

Suna sauƙa a Airport ɗin,
suka fito, a jere, yana gaba yana rike da hannun Sitti tana biye dashi a hankali tana taka step ɗin Jannart kuwa tuni itace a gaba.
Haroon ne wanda yake biye dasu a baya yana kallon yadda kakar tasu ke taka step da kuma yadda ɗan uwan nashi ke rike da hannun ta, murmushi yayi tare da jingina a ƙofar bakin jirgin cikin harshen larabci yace.
“Ko dai zaka goyeta ne ka sauƙar da ita”.
Sheykh bai kulashi ba, har saida suka sauƙo ya gyarawa Sitti tsayuwarta, kana ya miƙawa Jannart hannun Sitti alamun ta rike musu ita. Cikin jin daɗi Jannart ta riko hannunta tare da cewa.
“Ana Uhubbiki ya Sitti”. Cikin jin daɗi da son jikokin nata tace.
“Ana”. Sai kuma suka juyo suna kallon Sheykh dake tsaye cikin shiga ta al’farma shigar salihan bayi, wata dandatsetsiyar al’kyabbace mai masifar kyau ruwan ƙasace al’kyabbar sai surfani da aka sarrafa a jikinshi wanda yake da kalan gold, haka takalmanshi da hiraminshi duk masu ratsin Golding color ne, cikin tsananin jin daɗi Haroon ya fara sauƙowa daga step ɗin, yana kallon ɗan uwan nashi manda suke sa’anni, ruggume juna sukayi, cikin jin daɗi Haroon yace.
“Marhabin da zuwa Al’Sheykh, ya gida?, ina ƙannena? Yaya jikin Ya Jafar? Ya Hajja Mama da kowa da kowa.”
Kwaɓe fuska ya ɗanyi tare da janye jikinshi daga na Haroon cikin sanyinshi yace.
“Duk in kana son ganinsu kaje Nigeria zaka gansu, kana nan kullum sai yawo a jirgi kamar turuwa a daji, duk ƙasashen duniya ka gama zagayesu”.
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
“To ai dama na sani bakinka ɗaya da Umaymah’nka, zan koma ne in sha Allah, zan koma inyiwa ƙasarmu aiki, suma ai suna buƙata na”.
Fuskarshi ya ɗan kauda tare da cewa.
“Da yafi kam”. Juyowa sukayi jin Sitti na cewa.
“Kai Haroon ku taho mu tafi, ka tsareshi da surunka tun daga nan ko?”.
murmushi Haroon yayi kana ya nufi inda take tare da cewa.
“Oyoyo My Sitti”. Kai ta juya tare da cewa.
“Rabu dani ba kaga ɗan uwanka ka shareni ba”.
Ruggumeta yayi ta baya tare da cewa.
“Na isa in share uwar gida ran gida a gidan Sarki Jalaluddin”. Jannart ce tai dariya tare da cewa.
“Sitti karki yadda da daɗin bakinshi”.
Hannunshin yasa ya ɗan dungure kan Jannart tare da cewa.
“Kishi ko dan kinga gani ga uwar gida”.
murmushi Jannart tayi tare da jan hannun Sitti sukayi gaba, shi kuwa Haroon baya ya dawo ya saita da Sheykh suka fara tafiya a jere,
duk wanda yaga salo da tsarin tafiyar Sheykh zai gane cewa jini na sarauta na gudana a jikinshi, zai kuma gane nitsuwa ta addinin musulunci da kamala da haiba na hasken imanin ya game jiki da zuciyarshi.

A haka suka jera suna tafe, suna hira wacce ƙarfinta duk Haroon ke yinta.
Suna tafiya kaɗan.

Nan suka samu wasu irin zafafan tsala-tsalan motoci masu masifar kyau da tsada, suna jere a ƙalla sun kai goma sha biyu, motocine masu azabar kyau da sabunta da sheƙi da kyelli suna jere.
Kana ga kekkyawa fararen larabawa yan uwa da abokai
Da sauri suka rinka ɗan rusunawa suna, gaidasu Sitti da jikokinta, wani cikinsu ne da yake jikin wata dan datsetsiyar mota ƙirar Mercedes Benz maybach Exelero wacce kuɗinta zai kai kimanin $8 million dollars.
Motace mai masifar kyau da tsada, tana da inƙancin da ko bilet baya shigarta. Bisa dukkan alamu kuma sabuwa ce dal.
Direban dake jingine da ita ne yayi maza ya budewa Sitti bayan ta, a hankali suka ƙaraso gaban motar gaba ɗaya ma’akatan sunyi musu ƙawanya, cikin so da ƙaunar jikokin nata, ta yiwa Sheykh nuni daya fara shiga, ba musu kuwa ya shiga, motar, kana itama ta shiga sannan Haroon ya shiga, ya zamana sun sata a tsakiya,
Jannart kuma gaba ta shiga gefen drivern, suna gama shiga aka maida ƙofofin motar aka rufe.
Kana duk sauran hadiman suka shishiga motocin.
Kana suka fara tafiya a jere-a jere, tafiya sukeyi cikin salama da nitsuwa da bin doka da ƙa’idar tuƙi, kai tsaye suka wuce tushen ahlin nasu.

Wanda kafin su zoma, duk labarin zuwansu ya riski al’ummar family, kamar yadda aka saba, haka aka shirya musu tarba ta musamman an gyara sashin na musamman wanda nanne masaukin Sitti asali kuma sashin mahaifiyartace, anan cikin sashin kuma duk ahlinta da zaizo daga ƙasar Kautal nanne masauƙinshi, kuma kullum hadimai da bayin dake kula da wannan wurin suna nan suna tsabtace wurin. Suna isa fadar mai darar Sheikh Aliyu da kanshi ya fito tarbar babbar yayarshi wacce take a madadin uwa a gareshi a yanzu.

A wani falo da yafi dacewa da a kirashi al’jannar duniya, suka haɗu, a hankali Sheykh Aliyu ya ɗaga hannunshi alamun dakatar da ko wanne hadimi, a tare suka rusuna tare da komawa baya gaba ɗaya su.
Da sauri ya karaso gaban Sitti Ruggumeta yayi irin ruggumarsu ta jinin larabawa,
murmushi mai cike da jin daɗi ƙauna haɗida bege Sitti tayi tare dasa hannunta tsakiyar kanshi tace.
“Masha Allah, ɗan uwana na sameku lfy?”.
Saketa yayi tare da ruggume Sheykh yana murmushi tare da cewa.
“Alhamdulillah yar uwata, Barka da zuwa lfy”.
Cikin kula da zaƙuwa tace.
“Yaya jikin Baba”.
Murmushi ya kumayi still yana ruggume da Sheykh yana shafa bayanshi, yace.
“Alhamdulillah jikin baba da sauƙi kewarkice tafi damunshi”.
Sai kuma ya kalli Sheykh bayan ya sakeshi yace.
“Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero, barka da zuwa Doctor, ya gida ina Jafar da ƙannenka”.
Cikin son dottijon Sheykh ya ɗanyi wani ɗan guntun murmushi wanda shima sai yayi tsawon lokaci bai yishiba, cikin sassanyan murya yace.
“Suna lfy, sun gaidaka”.
Haroon ya tura baki tare da cewa.
“Wato mu ko ƴar ruggumar ma ta zumunci baza’ayi manaba, dan mu mun dade, nima zamu koma ƙasarmu mu rinƙa kawo muku ziyara jifa-jifa dan naga baƙi farinjini garesu a ahlinmu”.
Dariya sukayi baki ɗayansu,. Yayinda duk mgnar da sukeyi da harshen larabci sukeyi.

Wani faffaɗan corridor mai girma suka ratsa, wanda suka riski wani babbanshi na musamman, inda gaba ɗaya yayan family suke nan zaune dan mahaifin nasu a tsakiyarsu.
Wanda yake tsakiyar gatan duniya, farin dattijone wanda tsabar tsufa har ya juye ya koma tamkar ƙaramin yaro, ya ƙanƙance, yana hango Sitti, ya rinƙa sakin murmushi tare da miƙa mata hannunshi alamun tazo.
Da sauri ta nufi inda yake su Sheykh na biye da ita a baya, yayinda duk sauran mutanen ketayi musu barka da zuwa.
A gaban tsohon ta rusuna, tare da sunkuyowa, hannunshi ya saka bisa kanta yana jero mata addu’o’in da sanya mata al’barka, ita kam sitti da sauran ƙannenenta wanda a ƙalla sun kai arba’in sai Amin Amin suke amsawa,
Koda ya gama da Sitti jawo Sheykh yayi ya manna kanshi da cinyarshi,
Shikuwa Sheykh. Motsoshi yayi da kyau Cikin wani irin mashahurin daɗin da sai in yana gaban tsohon nan yakejin daɗi yasa hannunshi biyu ya kamo hannun dattijon ya ɗaura tsakiyar kanshi kana ya ƙara manna kanshi da cinyar tsohon tasbihi yakeyiwa Allah mai rayawa mai kashewa.
Ya sani shi kanshi da macece shi da yanzu yanada ya budurwa amman gashi wai a gaban kakan mamanshi, ga kuma kakar tashi da sukewa kallon tsohuwa itama gata gaban mahaifinta wannan abu shine abu ɗaya da yake sashi kuka muddin yana gaban tsohonda kullum in yazo irin gaisuwar da sukeyi kenan.
Shi kuwa Sarki Abdulkareem cikin rawan jiki irin na tsoffi yake shafa kan Sheykh tare da kallon taron ahlin naahi cikin muryarsa da bata fita sosai yasa suke sanƙala mishi na’urar ɗaga sauti a jikin alkyabbarsa, shiru sukayi gaba ɗayansu suka dakata da ruggume-ruggumen da sukewa Sitti,
Cikin rawan muryan da alamu tsohon kuka yakeyi a hankali yace.
“Ku bashi dukkan kulawarku, domin yana cikin Magauta, yanada tarin ƙunci da ƙuna a rayuwarshi, matsalolin rayuwar duniya sun mishi ƙawanya, saukinshi ɗaya Allah yayi mushi dafa’i da hasken imani da riƙo da ibada, damuwar tana daƙushe duk wani farin cikin rayuwarsa rashin fara’a ba izza bace damuwace, yana cike da al’hinin kula da ahlinshi,”.
Shiru ya ɗanyi tare da zubawa gaba ɗaya ahlin nashi idanu, sawon wasu daƙiƙu shiru falon babu sautin komai sai sassanyan sautin shessheƙan kuka da Sheykh a hankali, sai kuma sautin ƙaran A/C.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button