GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Shi kuwa Sheykh a hankali yace.
“Toh Umaymah a hakan ta yaya zan tozarta mahaifiyar Affan wanda duk munin halinta uwa dai uwace.”
Cikin rauni Umaymah tace.
“Wannan hakane Jazlaan amman Hajia Mama tanayi mana illa a rayuwa”.
Sosai jikin Haroon yayi sanyi.
Shi kuwa Sheykh Jalal ya kalla tare da cewa.
“Kaje Valli ka taho da Dr Kabir”.
Jiki a mace Jalal yace to kana ya miƙe ya fita.

Umaymah na biye dashi a baya, har taje bakin ƙofar fita a hankali yace.
“Ayyah Umaymah Ɗiyar taki ta kawo min ɗiyar tawa mana in ganta”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Toh”.
Shi kuwa Haroon da sauri yace.
“To bari in baka wuri dan nasan dai uwar ɗiya za’a gani ba ɗiyaba”.

A hankali yace.
“Mutun da abinsa”.
Dariya Haroon yayi kana ya nufi ƙofar da zata sadashi da Garden.

A hankali ta turo ƙofar Bedroom ɗinsa.
Tare da cewa.
“Assalamu alaikum”.
Cikin wani irin happy yace.
“Wa alaikissalam”.
sai kuma ya juyo ya fuskanceta tare da buɗe mata hannunshi.
Cikin sauri ta faɗa jikinshi ruggume da Afreen haɗe su yayi ya ruggume tare da cewa.
“Alhamdulillah ya Allah ka tsare min ahlinna ka cika mana farin cikinmu”.

“Amin ya Allah”. Ta faɗa a hankali sai kuma ya jawo hannunta suka zauna a bakin gadon.
Cikin narke fuska yace.
“Nayi fushi Aish tun ɗazufa na aika kizo baki zoba sai yanzu”.
Cikin sanyi tace.
“Ayyah Malam sallan la’asar nakeyi”.
Cikin sauri ya kalleta tare da cewa.
“Kai haba dai Aish da gaske shine baki gaya minba yaushe kika fara salla”.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Yoh ai dama ina salla”.
Lakace hancinta yayi tare da cewa.
“Batun gsky dai my dear yaushe kika samu tsarki?”.
Cikin nitsuwa tace.
“Yau da safe, nai wonka naci gaba da salla tunda naga jinin biƙin ya ɗauke na samu tsarki”.
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
“Masha Allah, jego yayi kyau kenan Boɗɗo na, dama wasu matan kafin satin sunama sun samu tsarki sun fara salla, kinga kema kina ɗaya daga cikinsu wasu kuma sai anyi arba’in ma, wasu har hamsin suna likin.
Koda yake ke dama al’adarma kwana uku kikeyi ko”.
Kai ta gyaɗa mishi.
Hannunshi ya cusa ƙasan pillow’nshi tare da zaro key ɗin sabuwar mota dal a leda.
Kamo hannun ta yayi ya danƙa mata key ɗin tare da cewa.
“Al’ada kwana uku baƙi kwana bakwai kai naji daɗi na, na more”.
Da sauri ta buɗe tafin hannunta tare da kallon key ɗin sai kuma ta lumshe idonta jin ya manna mata tattausan lips ɗinsa a goshi ya sake mata sassayan kiss.
Tare da cewa.
“Taki ce motar sai dai bani son kiyi tuƙi nafi son a jamin ke, sai daifa bana miji zai jamin keba.
Sara taki zata zama yar rakiyarki mai jan mota da tayaki kula da Babynmu, duk inda kuke in bana kusa daku.
Gimbiya Aminatu zata bamu wata mai girki”.
Cikin wani irin farin cikin ta ruggumeshi gam-gam a jikinta.
Da sauri yace.
“Wayyo Aish zaki danne Mimi na”.
Da sauri ta kwantar da Afreen gefe, kana ta faɗa jikinshi ta rungume shi.
Murmushi yayi mai cike da farin ciki cikin wasa yace.
“Zaki bani abin daɗi?”.
Da sauri tace.
“Ban workeba”.
Dariya mai ɗan sauti yayi tare da haɗe bakinsu wuri guda.

A part ɗinsu Jalal kuwa.
Yah Giɗi Seyo Gaini ne zaune bayan duk sunyi wonka, sun saka sabbin kayan da Jamil ya zaro musu cikin durowarsa.

Cikin wani irin yanayin jin daɗin duniya da kuma bege da kewar iyaye da ƴan uwa wanda da sun cire tsammani.
A hankali Yah Giɗi ya kalli Jamil dake miƙo mishi turare yana cewa.
“Kai masha Allah sai kunga yadda kukayi kyau, farinku ya ƙara fitowa”.
Cikin rauni Giɗi yace.
“Dan Allah bawan Allah, nan ina muke ne? Kuma ina wanda muka dawo dashi? Sannan ina za’a kaimu? Wayasa aka fito damu?”.
Da sauri Jamil ya zauna gabanshi kamo hannun shi yayi a hankali yace.
“Nan kuna cikin Ɓadamaya ne, cikin masarautar Joɗa, wanda kuka dawo dashi kuma Yayana ne Affan ya tafi ƙofar matarshi.
Wanda ya taimake ku yasa aka fitar daku kuma babban Yayanane Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa.
Yana nan matarsa ta haihu yau akeyin suna. Sai in ya nitsu zaizo wurinku shi zai gaya muku ina za’a kaiku”.
Wasu irin hawaye ne suka tsunkowa Gaini murya na rawa yace.
“Alhamdulillah kowa yace yaya zaiyi ya manta da Allahu wahidun ƙahharar sarki buwayi gagara misali mai badawa mai hanawa mai raya mai kashewa mai kawo sauƙi cikin tsanani mai yaye tsananin duhu ya wanzar da haske”.
Ido Jamil ya zuba musu cike da so da ƙaunar su, sai kuma ya kalli Seyo da yake zubda hawaye cikin sanyi yace.
“Ko wanne hali ahlinmu ke ciki”.
Da sauri Jamil yace.
“Yanzu muje falo kuci abinci kunji dan Allah ku bar kukan”.
Kasan cewar ya haɗa su da Allah yasa ba musu suka tashi.
Amman badon hakaba farin cikin da suke ciki ya kori yunwa bare ƙishi.

A tsakiyar falon suka zauna.
Jamil da kanshi ya zuba musu abincin da Aunty Rahma ta kawo musu.
Sukaci suka sha.

Dai-dai lokacin kuma aka kira sallan magriba.
Nan sukayi al’wala kana Jamil ya jasu sukayi jam’i.

Shatu kuwa bata bar ɗakin Sheykh ba saida ya tafi masallaci.
Ta fito cike da farin ciki.
Aunty Amina da Khadijah da Umaymah da Hibba ta samu a falonta Umaymah ta miƙa wa key ɗin tare da cewa.
“Umaymah Yah Sheykh ya saya min mota”.
Cikin jin daɗi Umaymah tace.
“Masha Allah. Allah ya sanya al’khairi”.
Amin Amin sukace baki ɗayansu.
Kana duk sukayi al’wala haramar salla.

Ƙarfe goma da rabi.
Duk baƙi sun watse.
Sai su Umaymah da su Aunty Amina.
A falon Shatu suke suna hirarsu cikin salama Ummi na ruggumi da Afreen.
Umaymah kuwa na haɗawa Shatu tea da fifitashi da kyau.
Aunty Rahma kuwa kitso Khadija keyi mata.
Junainah da Ishma kuwa suna can babban falon da Hibba da Jalal.

Sara da Larai da indo hadimar Aunty Juwairiyya kuwa tattare kitchin sukeyi da kimtsa ko ina na gidan.

Sheykh kuwa a hankali ya jawo wayarshi daya tattare wacce yake waya da Hajia Mama da ita.
Kiranta yayi.
Tana amsawa yace.
“Ƴar ta mutu ko?”.
Wani irin gigitaccen tsaki taja tare da cewa.
“Inafa ta mutu na dai ji ta suma amman wannan Shegen yaron duk abinda nayi a kanshi ko matarsa yanzu dama yar tashi abun baya tasiri.
Sannan babban tashin hankali na, shima Sarkin al’adun suna bai dawoba.
Kuma wayarshi na shiga baya ɗagawa, tsorona kada dai sun ganeshi”.
Cikin sauya muryarsa ih zuwa muryar Jahan yace.
“A a ba dai kamashi ba kam, sai dai ko in yana jin tsoron amsa kiran nakine sabida kada kiyi mishi faɗa tunda ƴar bata rasuba kada kice bai iya aikinsa bane a ganina fa shine yasa baya amsa kiran naki”.
Cikin tashin hankali tace.
“Ni babbar matsala ma yau tunda gari ya waye hankalina yake a tashi zuciyata na tsinkewa gaba ɗaya tsoro ya rufeni ji nakeyi wani mugun abu yana tunkaro rayuwata, naje gidan boka kuma ya koroni shima sai tsalle yakeyi yana kaɗe jikinsa
Wai komai na gab da dawo mana”.
Murmushi mai cike da jin daɗi yayi a ransa yake zaton ko shiryace zata zo mata, haka yasa yace.
“Sai gobe zanzo muyi mgn in kaiki gidan wani sabon boka”.
Da sauri tace.
“To”.

Daga nan ya katse kiran.
Kana ya miƙe ya fito falo, a hankali ya kalli Jalal da Hibba tare da cewa.
“Jamil fa”.
“Yana Part ɗin mu”.
Jalal ya bashi amsa”.
To yace kana ya juyo ya kalli Yah Jafar da yanzu ya shigo kenan.
A hankali ya tsaya gaban Sheykh.
A hankali suka lumshe idonsu a tare, da sauri Sheykh da Jalal da Hibba suka matso kusa dashi sosai jin yana cewa.
“Jabeer zuciyata na tsinkewa tun jiya sai inji kamar wani abu zai faru”.
Cike da mamaki Jalal yace.
“Wlh nima tun jiya zuciyata ke tsinke kirjina yaita bugawa”.
Wani irin rumtse ido Sheykh yayi tare da cewa.
“Nima abinda naketa fama dashi kenan tun jiya, to da Aisha ta suma sai nai zaton ko abinne ke samin tsinkewar zuciya.
To kuwa still abin bai bariba saima ƙaruwar da yakeyi yana tsananta”.
Cikin sanyi Hibba tace.
“To kuyi ta addu’a hakama Umaymah da Mamma da Aunty Rahma sukace suna ji”.
Kai suka gyaɗa gaba ɗaya.
Hannun Yah Jafar ɗin Sheykh yaja suka nufi Part ɗin su Jamil.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button