GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Dai-dai lokacin kuwa motar Salmanu dake gaban motocin su Abboi ta kusa kai cikin matsarautar Joɗa bayan an wangale musu gate.

Wani irin rumtse ido da ƙarfi Ummey tayi tare dasa kanta bisa guiwowinta sabida wani irin masifeffen tsarawa da kanta yayi da azaban ƙarfi.

Kai tsaye bakin part ɗin su Sheykh Salmanu ya nufa dasu sai dai Motar Abboi da sauran duk a can baya bakin fada suka tsaya inda Bappa ya nuna musu.

Yadda suke ƙara kusanto Part ɗin su haka sarawa da bugun zuciyar da Ummey keyi yake ƙaruwa.

A can cikin falon Shatu ma, da sauri Umaymah da Mamma Suka kalli juna sabida masifar bugawa da ƙirazansu sukayi.

Sheykh kuwa da ƙarfi ya ruggume Shatu sabida ji yayi tamkar zuciyarsa zata faso ƙirjinsa ta fito woje.
Jalal da ke Part ɗin Yah Jafar da sauri ya rumtse idanunshi shida Yah Jafar ɗin.

Hakama Jamil dake tare dasu Gaini.

A hankali motocin sukayi parking.
Ummey kuwa wani irin ƙara rumtse idanunta tayi da masifan karfi.
Dedde kuwa a hankali ta buɗe ƙofar.
Ta sako ƙafarsa cikin shigarta ta al’farma.

Shi kuwa Al’ameen da sauri ya zagayo ya buɗe wa Ummey kofar tare da cewa.
“Ummey mun iso bismillah”.
Cikin tsananin danne sarawar da kanta keyi ta ɗago jajayen idanunta a hankali ta zuro ƙafafuwan woje.

Ras ras Din dab din dab haka zuciyarta ta bada wasu tagwayen bugu.
Da sauri tasa hannunta ta dafe ƙirjinta.
Dedde kuwa a hankali ta zagayo inda take.
Shi kuwa Al’ameen a hankali yace.
“Bismillah ku shiga ga ƙofar”.
A hankali Dedde tace to kana ta nufi ƙofar.
Ita kuwa Ummey cikin rawan jiki ta ɗaga ƙafarta ta dama ta ɗaura kan barandar tare da ƙara dafe ƙirjinta da rumtse idanunta sabida jujjuyawan da kanta ya fara.
Shi kuwa Al’ameeen bayansu yabi.

Shi kuwa Salmanu a hankali ya kalli Hafsi ƙanwar Shatu dake bin Khadijah.
Cikin yin ƙasa da murya yace.
“Ko in ɗagaki ne in kaiki”.
Cikin jin kunya tace.
“A a Yah Salmanu zan shiga da ƙafata”.

Su Bappa kuwa Sarkin ƙofa ne yayi musu iso zuwa cikin fada.

A hankali Dedde ta kai hannunta ta kama handil ɗin ƙofar falon ta murɗa tare da turawa kana tasa ƙafarta ta dama ciki bakinta ɗauke da sallama.

Aunty Rahma dake fitowa daga kitchen Junainah na biye da ita da sauri ta ɗan juyo ta kalli Dedde tare da cewa.
“Wa alaikassalam”.
Ta ƙarashe amsa sallamar tana matsowa dan ganin wani irin fitinenne kama da Dedde keyi da Shatu.

Da sauri ta juyo bayanta jin Junainah na cewa.
“Lah Oyoyo Dedde”.

Dai-dai lokacin kuma Ummey ta ƙarasa shigowa ciki wanda hakan yayi dai-dai da bugawar da kanta yayi wanda saida tayi sauri sa hannunta duka y ta damƙe kanta da masifan karfi tare da cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun”.
Da ƙarfi wanda haka yasa Dedde juyowa ta fuskanceta sanadin juyawar da Dedde tayi kuma ya bawa Aunty Rahma da Junainah damar ganin fuskar Ummey da kyau.
Wani irin sauri Junainah tayi ta nufi inda suke ganin yadda gaba ɗaya jikin Ummeynta yake karkarwa da tsuma.

Aunty Rahma kuwa cikin wani irin tsananin firgita da kaɗuwa ta zazzaro idanunta waje har kamar zasu faɗo.
Wani irin taku mai cike da firgici tayi tana matsowa gaban Ummey dake jujjuyawa tana mai-mai-ta.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani’imanwakil”.
Wani irin matsowa kusa da ita Aunty Rahma tayi tare da buɗe baki da ƙarfi tace.
“La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallama. Aunty Mamey!.”
Ta ƙarashe kiran da azaban ƙarfi da rakaɗi.
Ummey kuwa.
Kiranta da Aunty Rahma tayi yasata ƙara gigicewa.
Karkar haka jikinta ke rawa.
Cikin wani irin gigitaccen murya Aunty Rahma ta fara rabkawa ahlinta kira.
“Umaymah! Mamma Jazlaan ga Aunty Mamey ta dawo da izinin ubangiji Jazlaan, Jafar, Jalal, Jamil, Umaymah. Kuzo ga Aunty Mamey…”.
Wani irin azabebben zabura…!

Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k ne kacal zaki turo ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Normal group Kuma 300 zaki turo ta asusuna ɗin sai kuyi screenshort na Debit Alert din ku turo min ta whatsApp 09097853276.

                     By
         *GARKUWAR FULANI*

[4/2, 7:40 AM] +234 806 559 0880: Cikin tarin kaɗuwa Umaymah, Mamma, Ummi, suka kalli juna tare da yunƙura suka tashi a tare.
Sabida jin kalmar da Aunty Rahma ke mai-maita wa, da tsananin ƙarfi da karaɗi.
A guje suka nufo falon sabida jin yadda take ƙara auna musu kira babu ƙaƙƙautawa.

Jalal da Yah Jafar da Aunty Juwairiyya dake Part ɗin su kuwa, suma da ƙarfi suku mimmiƙe tsaye, tare da juyowa suka nufo Part ɗin Sheykhhhh.

Dedde kuwa da sauri ta matso kusa da Ummey da nufin sa hannunta ta tallabeta, cike da al’hini al’amarin.

Junainah kuwa da gudu ta iso gareta tare da da faɗa wa jikinta ta ruggume sawunta tare da sakin kuka da ƙarfi sabida ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwar.

Sheykh kuwa da Shatu kafin kiran Aunty Rahma tayi mgnarta ta forko ruggume da ita yayi da kyau tare da cewa.
“Uhmmm kin san ko wanni sirri nawa, har na aikina da yake sirri amman ni kin gaza fitowa fili ki nuna min waye Bappa a wurinki waye Abboi a gareki”.
Hannun tasa ta ɗan shafa sajenshi ta buɗe baki da nufin yin mgn kenan suka tsinkayo. Muryar Aunty Rahma.

Wani irin tsinkewa da bugawa zuciyar Sheykh tayi da masifar ƙarfi wanda hakan ya haddasa wata iriyar fitinenneyar karkarwar zuciya da jiki, da ƙarfi ya sake rumtse idanunshi tare da sa yatsunshi cikin kunnuwanshi ya jijjiga sabida jin abin yakeyi kamar gizo.

Junainah kuwa wani irin masifeffen kuka tasa mai cike da rauni tare da yayyarfa hannunta murya a hargitse tace.
“Wayyo Adda Shatu! Adda Shatu zo kiga Ummeyn mu bata da lfy Adda Shatuuuu”.
Tayi kiran da masifan ƙarfin.
Ganin yadda Ummeyn ta tureta tare da jujjuyawa a tsakiyar falon kamar irin wacce hajijiya ke juyawa haka take tafiya tangal-tangal.

Wani irin zabura Shatu tayi wanda yayi dai-dai da lokacin da Mamma da Umaymah da Ummi da suka fito yanzu suka haɗa baki wurin cewa.
“La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam”.
Sai kuma gaba ɗaya jikinsu ya saki wani irin masifeffen karkarwa da sakewa ya rufesu.
Suka kasa koda ɗaga sawunsu bare su matsa inda suke.
Sabida tsananin kaɗuwa.

Ita kuwa Shatu tsalle ɗaya tayi ana biyu sai gata a bakin ƙofar Bedroom ɗinsa.
Cikin gigita shima ya yunƙuro da ƙarfi ya mara mata baya, sabida yadda yake jiyo falon a hargitse.

Gudu ya farayi ganin yadda Shatu ta fice a guje sabida ihun Junainah da take jiyowa.

Da sauri Yah Al’ameen ya sako kansa cikin falon jin muryar Junainah da abinda take cewa.

Yah Jafar da Jalal da Aunty Juwairiyya na biye
dashi a baya.

Cikin matsanancin tashin hankali Shatu ke kallon Ummey dake tsaye acikin tsakiyar falon, tana me riƙe da kanta dake juya mata sosai, ko mai bibbiyu take ganinsa, hakan yasa numfashinta soma ƙoƙarin ɗaukewa, take kuma idanunta suka rufe rub, hakan yasa ta-ta-fi luuu zata faɗi.

Da wani irin sauri mai haɗe da gudu Shatu da hankalinta yakai ƙololuwa wajen tashi ta ƙarasa wajen da Ummeynta ke tsaye, hakanne kuma yasa Ummeyn ta faɗa jikinta.

Hannayenta duka biyu tasa ta rungume Ummeyn tare da fara jinjigata cikin kiɗima da gigita, cikin muryar kukan da yazo mata lokaci ɗaya ta shiga faɗin.

“Innalillahi Wa’inna ilahirraju’un.
Ummeyna Ummeyna maiya sameki? Ummey ki tashi dan Allah, ki buɗe idanunki!!!”.
Ta ƙare maganar nata cikin matsanancin kuka, tare kuma da sanya hannayenta ta shiga girgiza Ummeyn da ƙarfi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button