GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

GARKUWA COMPLETE NOVEL

Kana ita kuma ta koma cikin gida.

A cikin masarautar Joɗa kuwa.

Sai da akayi sallan isha kafin.
Su Haroon suka dawo gida.
Suna tafe,
Abba da Lamiɗo da Galadima, da Dr Aliyu da kuma Sarkin Shaɗi.
Suna biye dasu a baya.

Kai tsaye wucewa sukayi har bedroom ɗin Jabeer har yanzu bacci yakeyi.
Sai dai tunda lokacin salla yayi yaketa jin baccin ba daɗi sai dai kuma Allah bai bashi ikon farkawa ba.
Dubashi sukayi tare da ƙara shafa mishi wasu magunguna kana suka fita suka tafi.

Hakama Gimbiya Aminatu tazo itama har ɗaki sai dai samunshi yana bacci yasa ta tafi.

Bayan fitanta ba daɗe Barrister Kamal da ɗan sa Sulaiman sukazo.
Suma har ciki suka shiga suka dubashi.
Kana suka tafi.

A ranan a daren gaba ɗaya mutanen masarautar kowa yaji lbrin abinda ya faru.

A falon su Jafar duk sukaci abinci.
Ganin dare ya tsalane yasa Juwairiyya jan hannun Jafar suka tafi.
Jalal, Jamil, Ya Hashim kuma sukayi musu saida safe kowa ya tafi side ɗin shi.

Jakadiyarsu kuwa itama ta nufi sashinta,
Ya zama dagashi sai Haroon.

Sha biyu da rabi dai-dai na dare.
Haroon zaune kan wata doguwar kujera irin ta sarakuna dake cikin ɗakin.
Waya yakeyi da Jannart,
yana konce ne dagashi sai boxes.
Waya sukeyi irin ta mosoyan da shaƙuwarsu tayi yawa,
Wani irin miƙa yayi wanda gaba ɗaya gabban jikinshi suka amsa.
Cikin tarin kasala da masifeffen shauƙi yace.
“Wash Allah na”.
Cikin kashe murya da ta ingizo Bukatarsa tace.
“Ohhh sorry Ya Haroon meya faru gaya min me yasameka”.
Cikin sakaliyar murya yace.
“Haroon yunwa yakeji”.
Sam bata fahimci inda batunshi ya dosaba haka yasa cikin haɗa fuska tace,
“Ya Haroon ka dawo gida, shi Hamma Jabeer ba matace dashi ba, bare ya kula da cikinku, na kuma san in kuna Side ɗinsa ba wani zuwa wurin Aunty Juwairiyya zakuyiba, kuma itama fama takeyi da mijinta.
Ni gsky ka dawo Tsinako nasan Umaymah zata kular min da kai da kyau, ko kuma kazo Masarautarmu Leddi julɓe, nida Sitti mu kula da kai”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Masarauta Joɗo fa masarautace mai daraja, da karrama baƙo baki san asalin tarihin inda masarautar tasamu suna Joɗa bako.
Baby kada ki damu kular da muke samu ko sarki mai mata huɗu da kwarkawara biyar baya samu.
Tako wani sashi na gidan abinci hadimai ke kawowa Side ɗin Sheykh a ƙalla wani lokacin kusan abinci kala goma muke riska, kinsan fulani ba marowata bane.
Kawai matsalar wannan yunwar rashinki ne, a kusa yasa nake jina ina tashi sama kamar doki”.
Cikin kunya da kauda zancen tace.
“Ya jikin Hamma Jabeer shugaban tuzuran ƙasar mu?”.
A hankali ya juyo kanshi ya kalli bisa makeken gadon da Jabeer ke kai.
Da sauri ya katse kiran bayan yace mata.
“Ina zuwa”.
Kan gadon ya nufa, jabeer ɗin yana ƙoƙarin tashi zaune.
Hannunshi daya miƙa zai taimaka mishi, ya buge cikin haɗe fuska yace.
“Yanzu ƙarfe nawa?”.
Wayarshi dake hannunshi ya duba cikin zuba mishi ido yace.
“Ƙarfe ɗaya dai-dai”.
Cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi kuka yace.
“Shine ka barni ina bacci kamar kafurin da bashi da addini.
Anyi sallan bamgrib baka tasheniba, anyi Isha’i baka tasheniba, daga wannan masifeffen bacci mara daɗi mai cike da mafarkai marasa daɗin da nasan rashin yin salla a lokacin sane ya jazamin su.
Iya wunin yau duk so kuke kuyi min asarar lokuta masu muhimmanci da daraja, kun sani na makara la’asar da magriba hakama isha.”
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye,
Tare daci gaba da cewa.
“Da fari ansa ni na tsaya gaban jama’a da baiyana surata,
Aka ɗora min da duka kana, akasa na makara sallan la’asar,
Yanzu kuma mangriba da isha’inma kun barni ina baccin asara na makara, sabida baka san darajar yin salla a cikin jam’i da kuma yin ta cikin lokacin ta ba ko?”.
Cikin taɓe baki Haroon yace.
“Kasan ai ni ba musulmi bane, ban san komaiba”.
Harara ya dannawa Haroon tare da cewa.
“Kai ka gayawa kanka, Ni bana kafurta mutum, abinda na sani dai kai tsarin yahudu da nasarane,
To bari kaji, Ni bani da laifin komai sabida bacci nakeyi, mai bacci kuma al’ƙalami ya sauƙa kansa har sai ya farka.
Kai dake ganina ina bacci lokacin salla yayi idonka biyu baka tasheniba haƙƙin a kanka ya rataya.”
Ya ƙarishe mgnar yana shiga bathroom tare da cewa.
“Ka cire idonka a kaina banza mai kallo kamar mayun wancan garin mugayen”.
Murmushi Haroon yayi tare da komawa ya zauna bisa kujerar.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wonka ya kumayi da ruwan ɗumi,
kana ya kimtsa cikin irin suturun da yake ta’ammali dasu, in yana gida.
kana ya ɗaura wata farar jallabiya kai.
Sannan ya fito bayan ya shafa mai ya fesa turare.

Yana fita ya fara ramuwar sallan daya wuceshi yana bacci.

Haroon kuwa falo ya fita abincin da yasan zai iya ci ya kawo mishin

A ƙalla awa ɗaya yayi kafin ya tashi kan sallayan
Gaban gadonshin ya dawo ya zauna bisa tattausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a wurin mai kalar Sky blue and white.
Sosai yaji daɗin jikinshi, sai dai har yanzu yana jin raɗaɗin bulalin.
Tea kawai ya iya sha.
Kana a hankali yace wa Haroon.
“Canza min beshit ɗin nan da blanket ɗin.”
Hararanshi Haroon yayi tare da cewa.
“Zan koma, yaseen na gaji da mulkinka da sarautar da kake ji dashi. Ji yadda ka medani tamkar wani bawanka ko hadimin gidanku, kuma duk abinda zanyi maka sai ka cini gyara, mutum ba’a iya mishi sai masifa kake min kamar dai nine nace a zaneka”.
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye tare da gimtse dariyarshi, sabida ganin kallon da Jabeer ke mishi.
A haka dai ya sauya komai na gadon kafin suka, hau suka konta.
Tsaki Jabeer yaja tare da cewa.
“Ni dama ka tafi wancan ɗakin sabida zancen gsky kasan ni bana son takura.
Sabida zaka hanani sakewa yadda nakeso”.
Cikin gajiya Haroon yace.
“Allah babu inda zan fita inje”.
Da haka dai Haroon yayi bacci.
Shi kuwa Sheykh Jabeer karatu yayi tayi har biyu da rabi tayi kana, ya buɗe tafin hannunshi yayi addu’o’in bacci.
Falaƙi 3 Nasi 3 ƙulhuwa 3 Ayatulkursi’u 1 kana amarrasulu 1 tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikinshi.
Kana ya kuma yi. Haka ya tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikin Haroon Wanda tuni ya ɓingire,
Shi kuwa Jabeer wannan al’adar rayuwarsa ce daya saba, kan Jalal da Jamil sabida suma haka suke bingirewa, shikeyi tofi ya shafa musu.

Washe gari Lamiɗo baiyi zaton Jabeer zai samu fitowa masallaci ba,
Shiyasa limamin dake jansu salla in baya nan ya fito ya jasu salla,
yayinda Jabeer ke cikin sahun forko.

Wannan yasa mutane sukayi zaton ciwon ne yayi tsamari bai samu ya fitoba.
Ana idar da salla kuma ya fito yayi cikin gida sabida.
Fushi yakeyi da wannan tsohon ya sani in ya tsaya kuma zai dameshi da wata falsafarshi da zaici karo da addini.

Ƙarfe takwas dai-dai. Barrister Kamal da Ya Jafar, da kuma Baba Basiru ne zaune dashi a falon shi.

Suna zaune anan Jalal ya shigo cikin yanayin damuwa yace.
“Hamma Jabeer, Umma na falo tazo dubaka da jiki.”
Cikin yamutsa fuska yace.
“Wacece hakan?”.
Cikin fusata Baba Basiru yace.
“Ashe uwarka ma bazaka santa ba, ina dai baka san wacece Umma ba”.
Wani irin kallon ido cikin ido Sheykh yayiwa Baba Basiru,
sai kuma ya ɗora ƙafarshi ɗaya kan ɗaya, cikin ƙasaita ya kalli Jalal tare da cewa.
“Mene Umman!?”. Ya sani sarari Gimbiya Saudatu ake cewa Ummu .
Gyara tsayuwa Jalal yayi tare da gyara zaman belt ɗin ƙugunshi yace.
“Matar tsohon Galadima marigayi, Baba Muhammad ce Ummar Gimbiya Saudatu.”
Da sauri Baba Basiru yayiwa Jalal daƙuwa tare da cewa.
“Kan uwarka hegen yaro ɗan shila”.
Shi kuwa Jabeer ƙafarshi ya fara kaɗawa.
Barrister Kamal kuwa ido ya zubawa Fuskarta Jabeer da Jalal. Cikin sanyi da tausasan laffuza yace.
“Jabeer tashi muje ka gaisa da ita tunda ta taso tazo har nan dubaka da jiki”.
Kanshi ya gyaɗawa Barrister Kamal ɗin wanda suke cewa Baba Kamal wanda yake mahaifin Sulaiman, sa’an Jabeer.
Da hannu yayiwa Jalal alamun yaje yace, yana zuwa.
Shi kam Baba Basiru bayan Jalal yabi.
A babban falon suka zauna shida Gimbiya Saudatu da Laminu da kuma Baba Nasiru.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137 138 139 140 141 142 143 144 145 146 147 148 149 150 151 152 153 154 155 156 157 158 159 160 161 162 163 164 165 166 167 168 169 170 171 172 173 174 175 176 177 178 179 180 181 182 183 184 185 186 187 188 189 190 191 192 193 194 195 196 197 198 199 200 201 202 203 204 205 206 207 208 209 210 211 212 213 214 215 216 217 218 219 220 221 222 223 224 225 226 227 228 229 230 231Next page

Leave a Reply

Back to top button